Tsohuwar tauraruwar fina-finan Hausa Ummi Zee ta bayyana yanda wani mutum da ta yarda dashi ya yaudareta, Ummi ta bayyana cewa duk girman mutum idan bashi da Adalci to akwai matsala, bashi da gaskiya kenan.
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Ga sakon data rubuta kamar haka:
“ADALCI wani hali ne da Allah yake bawa mutane masu gaskiya kawai.duk Wanda bayi da ADALCI to mutum ne mara gaskiya koshi wanene,shiyasa ma musulunci yace ana iya bawa arne shugabanci in har yana da ADALCI.ammah yanzu mutane masu ADALCI suna da wuyan samu dan yanzu ba gaskiya a duniya..wani ne yamin rashin ADALCI da banji dadinsa ba Wanda harta kai ga na dena ganin girmansa bayan kuma ada ko magana ya gayamin ina amfani dashi.rashin adalcin dayamin shine na samu matsala da abokinsa kuma abokin nasa shi yake cuta na kullum wai ammah idan zai sasanta mu sai ya dinga bin bayan abokin nasa ni kuma ya dauramin laifi .tun daga nan sai na gane shima munafuki ne mara gaskiya .sai na hada dagashi har abokin nasa ,nasa su a kwandon shara dan naga dukkansu munafukai ne mara sa gaskiya dan dama hausawa sunce sai hali yazo daya ake ABOTA ……”
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});