fbpx
Thursday, June 8
Shadow

Yanzu-Yanzu: Rikici ya barke a APC, Hankalin Tinubu ya tashi bayan da shugaban APc yace Sanata Ahmad Lawal ne zabin shugaba Buhari

Ana can jam’iyyar APC ba zaman lafiya bayan da shugaban jam’iyyar,  Sanata Abdullahi Adamu ya bayyana kakakin majalisa, Sanata Ahmad Lawal a matsayin zabin da aka yi wanda ba sai an yi zabeba ya zama dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar tasu.

 

Adamu ya bayyana hakane a wajan taron kwamitin masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC dake gudana a Abuja.

 

Saidai yace duk da zabin na Ahmad Lawal sauran ‘yan takarar zasu iya tsayawa a fafata a zaben fidda gwanin.

 

Yace ya zabi Ahmad Lawal ne bayan tuntubar shugaban kasa, Muhammadu Buhari.

Karanta wannan  Ina goyon bayan cire tallafin man fetur>>Peter Obi

 

Dan sauke manhajar hutudole a wayoyin ku. Sai a bi wannan link din na kasa:

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *