fbpx
Saturday, June 10
Shadow

Zamu Kubutar da wadanda ‘yan ta’adda suka sace daga jirgin kasan Kaduna-Abuja>>Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin tarayya ta bayar da tabbacin kubutar da wanda ‘yan Bindiga suka sace daga jirgin kasan dake jigila tsakanin Kaduna zuwa Abuja.

 

Ministan sufuri, Rotimi Amaechi ne ya bayar da wannan tabbaci inda yace ba zasu yi kasa a gwiwa ba har sai sun ga an kubutar da mutanen.

 

Ya bayyana hakane ranar Alhamis a wajan ganawa da manema labarai a babban birnin tarayya, Abuja.

 

Ya bayyana cewa, ma’aikatarsa na ganawa da jami’an tsaro kan ceto mutanen, Saidai yace ba za’a fadi irin shirin da ake ba dan kada hakan ya kawo matsala.

 

Wasu ‘yan uwan wadanda aka sace din dai sun je wajan taron inda suka fara Zanga-Zanga.

Dan sauke manhajar hutudole a wayoyin ku. Sai a bi wannan link din na kasa:

Talla: Danna nan dan samun gagarumar kyauta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *