Friday, April 25
Shadow

Zan kori duk ministan da baya aiki yanda ya kamata>>Shugaba Tinubu

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, zai kori duk ministan da baya aiki yanda ya kamata.

Tinubu ya bayyana hakane a ganawar da yayi da kungiyar dattawan Arewa ta ACF da yammacin ranar Alhamis.

Yace zai ci gaba da yin aiki iya kokarinsa dan ci gaban Najeriya.

Ya bayyana cewa, yana godewa ‘yan majalisar zartaswarsa kan kokarin da suke amma zai rika dubawa yana tankade da rairaya dan gano wanda basa aiki yanda ya kamata dan canjasu.

Karanta Wannan  Tunda ake Najeriya ba'a taba yin shugaban kasa me karfin Gwiwa kamar ni ba, na yi abinda shuwagabannin baya suka ji tsoron yi, watau cire tallafin man fetur ba tare da tunanin sake zabe na ba>>Tinubu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *