Friday, December 5
Shadow

Ƙungiyar shugabannin Arewa ta nemi Tinubu ya sauya shugabannin sojin Najeriya

Wata ƙungiyar shugabanni a arewacin Najeriya ta nemi Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya sauya salon yaƙi da matsalar tsaro bayan harin da Boko Haram ta kai a jihar Borno.

Ƙungiyar Northern Ethnic Nationality Forum ta siffanta lamarin da “bala’i” saboda yadda hare-haren masu iƙirarin jihadi ke hana ayyukan noma da kasuwanci, da kuma garkuwa da mutane da ‘yanbindiga ke yi don neman kuɗin fansa.

A ranar Asabar ne mayaƙan Boko Haram suka kashe sama da mutum 60 bayan harin da suka kai a jihar Borno.

A yau Lahadi ne ƙungiyar ta nemi a naɗa sababbin shugabannin rundunar soja da kuma yi wa majalisar ministoci ta gwamnatin APC garambawul.

Karanta Wannan  Nifa a wajena Musulmai da Kiristoci Shedan suke Bautawa>>Inji Ibrahim El-Rufai

Kazalika, sun nemi Shugaba Tinubu ya sanya dokar ta-ɓaci a yankin domin yaƙi da matsalar tsaron da ta jawo kashe dubban mutane, musamman a yankin arewa maso yamma.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *