Thursday, February 5
Shadow

Ƙungiyar shugabannin Arewa ta nemi Tinubu ya sauya shugabannin sojin Najeriya

Wata ƙungiyar shugabanni a arewacin Najeriya ta nemi Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya sauya salon yaƙi da matsalar tsaro bayan harin da Boko Haram ta kai a jihar Borno.

Ƙungiyar Northern Ethnic Nationality Forum ta siffanta lamarin da “bala’i” saboda yadda hare-haren masu iƙirarin jihadi ke hana ayyukan noma da kasuwanci, da kuma garkuwa da mutane da ‘yanbindiga ke yi don neman kuɗin fansa.

A ranar Asabar ne mayaƙan Boko Haram suka kashe sama da mutum 60 bayan harin da suka kai a jihar Borno.

A yau Lahadi ne ƙungiyar ta nemi a naɗa sababbin shugabannin rundunar soja da kuma yi wa majalisar ministoci ta gwamnatin APC garambawul.

Karanta Wannan  Ji Yanda 'Shugaban 'yansandan Najeriya ya karawa Dogariyarsa mace mukami ba tare da ta rubuta jarabawar karin mukamin ba'

Kazalika, sun nemi Shugaba Tinubu ya sanya dokar ta-ɓaci a yankin domin yaƙi da matsalar tsaron da ta jawo kashe dubban mutane, musamman a yankin arewa maso yamma.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *