
Matsalar rashin kudi ta fara haifarwa da ‘yan Najeriya tabin kwakwalwa, cewar likitan kwakwalwa
Matsalar rashin kudi ta fara haifarwa da 'yan Najeriya tabin kwakwalwa, cewar likitan kwakwalwa.
Likitan kwakwalwa Ben Arikpo ya bayyana cewa matsalar karancin kudi da tsadar man fetur ta fara haifarwa da 'yan Najeriya tabin kwakwalwa.
Inda ya bayyana cewa ya kamata al'ummar Najeriya su san yadda zasu cigaba da tafiyar da al'amuransu koba tallafin gwamnati.
Domin karancin kudi da tsadar man fetur ba karamar barazana bace ga lafiyarsu.