Wednesday, August 12
Shadow
Kawar Amani, Maruma ta zargi cewa, Amani da aurenta take yawace-yawace

Kawar Amani, Maruma ta zargi cewa, Amani da aurenta take yawace-yawace

Duk Labarai
Wani comment da ake alakantawa da Maruma, kawar Amani tsohuwar Budurwar Bilal Villa ya karade kafafen sada zumunta. A comment din an ga Maruma ta rubuta cewa wai Amani na da aure a Saudiyya amma ta baro mijin ta taho Najeriya take yawon Tazubar. Saidai wannan lamari ya zowa mutane da mamaki saboda musamman karancin shekaru na Amani inda wasu da yawa ke cewa basu yadda ba. Ana cikin haka kwatsam sai kuma ga wata murya itama ta bayyana inda take cewa, Amani ba a Saudiyya ta yi aure ba, a Nijar ne. Zuwa lokacin hada wannan Rahoton dai ba'aji ba daga bakin amani. https://www.tiktok.com/@call_me_notification001/video/7672703537205529863?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7672703537205529863&source=h...
‘Yansanda sun kama Malaman jami’a saboda sun ce zasu je yajin aiki

‘Yansanda sun kama Malaman jami’a saboda sun ce zasu je yajin aiki

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Imo na cewa, 'yansanda sun kama malaman jami'ar Imo State University (IMSU) dake karkashin kungiyar malaman jami'a ta ASUU dan sun bayyana cewa zasu je yajin aiki. Rahoton yace an kamasu ne bayan wani shiri da aka yi dasu a wani gidan rediyo na jihar inda suka bayyana aniyarsu ta shiga yajin aiki saboda rashin cika alkawarin da Gwamnati ta musu. Malaman sun bayyana cewa ya kamata alkawarin da gwamnatin tarayya tawa jami'o'in Najeriya ya hada hadda jami'o'in Jihohi. Daga cikin wadanda aka kama hadda shugaban kungiyar ASUU din na jihaa, watau Chairman, Stephen Oguji. Saidai Rahoton Vanguard ya ce daga baya an sakesu. Amma kungiyar ta ASUU tace wannan ba zai bata tsoro ba. Tuni dai kungiyar ASUU ta kasa ta sanar da cewa, zata bayar da kwanaki 14 a biya ...
Khadija Muhammad na ƙoƙarin tona asirin wani a Kannywood — amma ta ƙi bayyana sunansa!

Khadija Muhammad na ƙoƙarin tona asirin wani a Kannywood — amma ta ƙi bayyana sunansa!

Duk Labarai
Jarumar Kannywood Khadija Muhammad ta bayyana cewa tana ƙoƙarin tona asirin wani mutum a Kannywood da take zargin ya ƙi biyan ta hakkinta.Abin da ya ƙara ɗaukar hankalin mutane shi ne yadda ta yi wasu bayanai da suka sa mutane ke ƙoƙarin gano wanda take magana a kansa. Wasu ma sun ƙagu ta saka hotonsa ko ta ambaci sunansa, amma har yanzu Khadija ba ta bayyana sunan mutumin ba. Sai dai a cikin bayaninta, ta yi masa wata siffa mai ban dariya, inda ta ce “shi ya sa yake da ƙaton tumbi, ashe duk haƙƙinmu a ciki yake.” Ku a ganinku, ya kamata Khadija ta bayyana sunan mutumin da take zargi, ko ta nemi hakkinta ta hanyar da ta dace ba tare da tona sunansa a kafafen sada zumunta ba?
Kalli Bidiyon yanda shugaba Tinubu ke zuwa Ofis a kafa

Kalli Bidiyon yanda shugaba Tinubu ke zuwa Ofis a kafa

Duk Labarai
A jiyane dai labarai suka karade kafafen sada zumunta cewa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a kasa yake zuwa ofis daga gidansa a Villa. Shugaban hukumar tattara Haraji ta kasa, NRS, Adedeji ne ya bayyana haka a wata hira da aka yi dashi. A yau kuma sai aka tashi magoya bayan shugaban kasar suna yada Bidiyon da ikirarin cewa shine yake takawa da kafa zuwa ofishinsa. https://twitter.com/i/status/2086824986879119551