Wannan wasu 'yan Najeriya ne da ke sana'a a bakin titi a kasar Saudiyya.
An gansu suna guje-guje bayan da suka ji kukan motar jami'an tsaro kowa yana ta kansa.
https://twitter.com/i/status/2085462199254806885
Tsohon Mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya bayyana cewa, an masa kutse a asusun bankinsa an kwashe masa kudade.
Ya bayyana hakane a wata sanarwa da ya fitar ta bakin magana da yawunsa Frank Shu'aibu.
Atiku yace bayanan bankin nasa babu wanda ya san dasu amma sai gashi an kwashe masa kudade a ciki.
Yace idan mutum kamarsa za'a iya mai haka to lallai akwai matsala.
Wannan wata matashiyace da aka kama bisa zargin zuwa Asibitin Babura jihar Jigawa dan satar Jariri.
Tace daga Unguwar Kinkinau take a jihar Kaduna inda take ta rokon su rufa mata Asiri kada iyayenta su gani.
Ta bayyana cewa wai yaran idan suka daukesu tallafi za'a basu
https://twitter.com/i/status/2085621216040144943
Bidiyon wata damin Naira da aka gano a dakin wani me kudi ta dauki hankula sosai.
An ga kudin sun lalace sun zama gari, amma akwai wasu dalolin Amurka da basu lalace ba.
https://twitter.com/i/status/2085604424160813131
Tauraruwar fina-finan Hausa, Shetty ta cikin shirin wata shida ta bayyana a wani Bidiyo inda aka ganta da wata shiga wadda bata dace ba.
Da yawa sun rika bayyana cewa ba musulma bace saboda shigar bata dace da al'adu da addinin Arewa ba.
An dai dauki Bidiyon ne a wajan daukar fim din na wata shida.
Danna nan dan kallon Bidiyon
Tauraruwar Tiktok, Habiba Dorayi ta wallafa wani Bidiyon inda take rawa da kirjinta wanda ya dauki hankulan masoyanta.
https://www.tiktok.com/@habibadorayi/video/7670925115613351185?_r=1&_t=ZS-98g74E5iD0k
Farashin dala a kasuwar Chanji ta gwamnati a yauz Juma'a, 7 ga watan Augusta na shekarar 2026 ya kamane akan Naira ₦1,368.22 ne akan kowace dala.
Farashin dalar a kasuwar bayan fage ta garuruwan Kano, Abuja, Lagos da Fatakwal ya kamane akan naira ₦1,405 akan kowace dala.
Bidiyo sun karade kafafen sada zumunta inda aka ga wasu mata da suka je taron jam'iyyar APC a Kano, dubban matasa sun daka musu wawa.
A Bidiyon an ga matan zagaye da samari masu yawa.
Waji Rahoton yace hadda Teema Cool wadda tana gaba-gaba wajan goyon bayan Gwamnatin Gwamnan Kano, Abba Gida-Gida.
https://www.tiktok.com/@usersanikoki/video/7670981692068334856?_r=1&_t=ZS-98g05JH7QCA
https://www.tiktok.com/@abdurrazak.ishak/video/7670984517611457799?_r=1&_t=ZS-98g1HcIBzLs
https://www.tiktok.com/@teemahcool0/video/7671060799833574664?_r=1&_t=ZS-98g1h7Oj6lM
Saidai ta fito ta karyata cewa itace.
Rahotanni sun ce lamarin ya farune a Unguwar Kurna.
Rikici ya barke tsakanin Rahama Saidu me babban shago da yaran shagonta 3.
Rahama Ta zargi yaran shagon da yi mata sata.
Tace abaya 2 suka sace mata.
Ta wallafa Sunayensu a shafinta na sada zumunta inda tace yanzu basa aiki da ita.
A baya ta wallafa hadda hotuna da Bidiyon su kamar yanda suka yi zargi amma ta goge.
Saidai daya daga cikin wadanda ta kora daga aikin, ta fito ta musanta wannan zargi.
Tace abaya da tace sun bata sayarwa suka yi kuma an turawa Rahama kudinsu a asusun bankinta.
Ta yi zargin cewa, Sun bayyana wa Rahama Saidu cewa ba zasu iya ci gaba da aiki da ita ba saboda albashin da take basu yayi kadan
Shine ta fito da hanyar yi musu sharri.
Ta kuma ce tana bin Rahama Saidu Albashin watanni 2 bata biyata ba.
https://www.tiktok.com/@flowerbabyo1...
Wani magidanci a jihar Kaduna ya kai tsohuwar matarsa kotu saboda ta ki fita ta bar masa gida, Shekaru 2 bayan da ya saketa.
Mutumin wanda dan kasuwane me suna Dauda Dahiru ya kai tsohuwar matartasa karane kotun magajin gari dake Kaduna.
Da yake magana ta bakin lauyansa, Hassan Sadisu yace suna da 'ya'ya 5 mata da matar tasa da yaro namiji 1.
Yace a lokacin da ya saketa tana dauke da cikinsa shine yace ta zauna sai ta haihu, yace amma ta haihu yanzu shekara 2 kenan da sakin amma taki fita daga gidan.
Yace ya ma sayar da gidan sannan yace zai kama mata wani gidan saboda yara amma taki yadda.
Matar dai a nata martanin tace idan yana son ta tashi sai ya sai mata gida ko da me daki dayane ko kuma ya kama mata haya ya biya kudin haya na shekaru 5.
Saidai me shari'a, Mu’awiya...