Thursday, August 6
Shadow
Kalli Bidiyon: Rikici ya barke tsakanin Rahama Saidu me babban Shago da yaran Shagonta inda ta zargesu da mata sata

Kalli Bidiyon: Rikici ya barke tsakanin Rahama Saidu me babban Shago da yaran Shagonta inda ta zargesu da mata sata

Duk Labarai
Rikici ya barke tsakanin Rahama Saidu me babban shago da yaran shagonta 3. Rahama Ta zargi yaran shagon da yi mata sata. Tace abaya 2 suka sace mata. Ta wallafa Sunayensu a shafinta na sada zumunta inda tace yanzu basa aiki da ita. A baya ta wallafa hadda hotuna da Bidiyon su kamar yanda suka yi zargi amma ta goge. Saidai daya daga cikin wadanda ta kora daga aikin, ta fito ta musanta wannan zargi. Tace abaya da tace sun bata sayarwa suka yi kuma an turawa Rahama kudinsu a asusun bankinta. Ta yi zargin cewa, Sun bayyana wa Rahama Saidu cewa ba zasu iya ci gaba da aiki da ita ba saboda albashin da take basu yayi kadan Shine ta fito da hanyar yi musu sharri. Ta kuma ce tana bin Rahama Saidu Albashin watanni 2 bata biyata ba. https://www.tiktok.com/@flowerbabyo1...
Magidanci a jihar Kaduna ya kai tsohuwar matarsa kotu saboda ta ki barin gidansa shekaru 2 bayan ya saketa

Magidanci a jihar Kaduna ya kai tsohuwar matarsa kotu saboda ta ki barin gidansa shekaru 2 bayan ya saketa

Duk Labarai
Wani magidanci a jihar Kaduna ya kai tsohuwar matarsa kotu saboda ta ki fita ta bar masa gida, Shekaru 2 bayan da ya saketa. Mutumin wanda dan kasuwane me suna Dauda Dahiru ya kai tsohuwar matartasa karane kotun magajin gari dake Kaduna. Da yake magana ta bakin lauyansa, Hassan Sadisu yace suna da 'ya'ya 5 mata da matar tasa da yaro namiji 1. Yace a lokacin da ya saketa tana dauke da cikinsa shine yace ta zauna sai ta haihu, yace amma ta haihu yanzu shekara 2 kenan da sakin amma taki fita daga gidan. Yace ya ma sayar da gidan sannan yace zai kama mata wani gidan saboda yara amma taki yadda. Matar dai a nata martanin tace idan yana son ta tashi sai ya sai mata gida ko da me daki dayane ko kuma ya kama mata haya ya biya kudin haya na shekaru 5. Saidai me shari'a, Mu’awiya...
Kalli Bidiyon: Yanda ‘Yan mata ‘yan Kwallon Najeriya suke ta rawa a dakin canja kaya bayan nasarar kaiwa ga watan Quarter finals a gasar cin kofin mata na nahiyar Afrika

Kalli Bidiyon: Yanda ‘Yan mata ‘yan Kwallon Najeriya suke ta rawa a dakin canja kaya bayan nasarar kaiwa ga watan Quarter finals a gasar cin kofin mata na nahiyar Afrika

Duk Labarai
'Yan kwallo 'yan mata na Najeriya, Super Falcons sun rika tika rawa suna tsalle biyo bayan nasarar kaiwa ga wasan Quarter finals a gasar cin kofin mata na Afrika. Bidiyon rawar tasu ya karade kafafen sada zumunta inda ake ta tayasu murna. https://twitter.com/i/status/2085343660590145553
Kalli Bidiyon: Wata daliba dake rawa a wajan Bikin ranar Al’adu ta makarantar su data dauki hankula

Kalli Bidiyon: Wata daliba dake rawa a wajan Bikin ranar Al’adu ta makarantar su data dauki hankula

Duk Labarai
Wata daliba data yi rawa a wajan Bikin ranar Al'adu ta makarantarsu ta dauki hankula. Bidiyon ta tana kwarwaksa ya karade kafafen sadarwa inda akai ta bayyana mabanbanta ra'ayoyi akai. Inda da yawa ke Allah wadai da abin, wasu kuma na cewa, ba zasu bar diyarsu ta shiga irin wannan gasar ba. https://www.tiktok.com/@beesu_cinematic/video/7670687137469107463?_r=1&_t=ZS-98eueLJvCwH
Kalli Bidiyon: Ganin ‘yan Shi’a suna kade-Kade a makabarta wajan binne wadanda suka rasu a wajan tattaki ya dauki hankula

Kalli Bidiyon: Ganin ‘yan Shi’a suna kade-Kade a makabarta wajan binne wadanda suka rasu a wajan tattaki ya dauki hankula

Duk Labarai
An ga 'yan Shi'a na kida a makabarta wajan binne wadanda suka rasu a wajan Tattaki. Lamarin ya dauki hankula sosai inda ake ta bayyana mamaki. Mutane 5 ne dai suka rigamu gidan gaskiya a wajan Tattakin. https://www.tiktok.com/@_zainab_akeelah/video/7670640919330213141?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7670640919330213141&source=h5_m&timestamp=1786021265&user_id=7483197776647635989&sec_user_id=MS4wLjABAAAAN7fVbcc0mzRzgIxdVwTekj-Bzgfq381B8aILPWs15fqP6aFNZ5GwIpbLEwMTYvVW&social_share_type=0&utm_source=copy&utm_campaign=client_share&utm_medium=android&share_iid=7665740753532061457&share_link_id=f59cd2c4-6986-48e4-bfe0-dd7925e426aa&share_app_id=1233&ugbiz_name...
Kalli Bidiyon: Yanda matashi ya rika daukar mata a jihar Kaduna da suka je taron siyasa ana basu kudi

Kalli Bidiyon: Yanda matashi ya rika daukar mata a jihar Kaduna da suka je taron siyasa ana basu kudi

Duk Labarai
Wani matashi ya rika daukar mata Bidiyo da suka je taron Siyasa a jihar Kaduna aka basu Shinkafa. Matan dai sun rika kare fuskarsu basa son a daukesu amma yace dole su dauke su tunda sune ke saka mutane cikin wahala. Da yawa dai sun yaba masa kan hakan. https://www.tiktok.com/@a.adam001/video/7670149705153711361?_r=1&_t=ZS-98eJvJ5PNeT
Da Duminsa: Adam A. Zango ya kara aure

Da Duminsa: Adam A. Zango ya kara aure

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa Tauraron fina-finan Hausa, Adam A. Zango ya kara aure kwanaki kadan bayan rabuwa da tsohuwar matarsa, Maimuna. Wadda ya aura, Maryam Gombe ce ta wallafa labarin inda tace a yau an daura mata aure da baba Ado. Maryam tace duk wanda tawa laifi tana fatan ya yafe mata kuma tana fatan Allah ya basu zaman Lafiya. Hutudole ya dade da lura da cewa akwai soyayya tsakanin Adam A. Zango da Maryam. Domin a baya ta sassaka Hotuna da Bidiyon su tare. Maryam Dai ittace wadda Ordinary President Ahmad Isa yaso kaita kotu kara saboda zargin bata suna