Saturday, April 11
Shadow
Ji Sautin Murya: Tinubu ba kudi ya bani na masa yakin neman zabe ba, tunda na sanshi ba ko ruwan Fiya wata bai taba bani kudi na siya ba>>Inji Malam Nasiru Ahmad El-Rufai

Ji Sautin Murya: Tinubu ba kudi ya bani na masa yakin neman zabe ba, tunda na sanshi ba ko ruwan Fiya wata bai taba bani kudi na siya ba>>Inji Malam Nasiru Ahmad El-Rufai

Duk Labarai
Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana cewa, ba kudi Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bashi ya masa yakin neman zabe ba. Yace shi tunda yasan Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu bai taba bashi ko sisi ba ko da kudin siyen Pure Water. Yace amma ba zai iya rantsuwa akan sauran wadanda sukawa Tinubu yakin neman zabe ba amma shi dai ba'a bashi ko sisi ba. https://twitter.com/i/status/2042551635289739358
INEC ta tabbatar da David Mark a matsayin shugaban jam’iyyar ADC

INEC ta tabbatar da David Mark a matsayin shugaban jam’iyyar ADC

Duk Labarai
Lauyan David Mark, Realwan Okpanachi ya tabbatar da cewa a takardar rantsuwa da hukumar zabe me zaman kanta, INEC ta gabatarwa da kotu. Ta tabbatar da cewa, David Mark ne halastaccen shugaban jam'iyyar ADC hakanan Rauf Aregbesola shine halastaccen sakataren jam'iyyar. Ya bayyana hakane ga manema labarai bayan zaman kotun. A yanzu dai kotu ce za'a jira ta yanke hukunci kan karar. https://twitter.com/i/status/2042698761843912756
Ikon Allah: Kalli Bidiyon yanda Sojojin dake cikin tawagar yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu suka kaure da fada suna dukan Juna

Ikon Allah: Kalli Bidiyon yanda Sojojin dake cikin tawagar yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu suka kaure da fada suna dukan Juna

Duk Labarai
A yau ne shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya kai ziyara jihar Bayelsa. A cikin tawagar motocin dake masa rakiya, an ga wasu sojoji sun tsaya a hanya suna dambe. Bidiyon lamarin ya dauki hankula sosai a kafafen sada zumunta inda da yawa ke cewa hakan bai dace ba. https://twitter.com/i/status/2042690556531257589
Yanda aka shirya munafurcin Tsigeni a matsayin Gwamna da hadin Bakin Mataimakina, Gwarzo, dan ya gajeni>>Inji Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf

Yanda aka shirya munafurcin Tsigeni a matsayin Gwamna da hadin Bakin Mataimakina, Gwarzo, dan ya gajeni>>Inji Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf

Duk Labarai
Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya bayar da labarin yanda aka shirya munafurcin tsigeshi a matsayin Gwamna tare da hadin gwiwar mataimakinsa da ya sauka, Gwarzo. Gwamnan yace an shirya tsigeshi ne sai kuma Gwarzo ya maye gurbinsa. Yace amma sai Allah bai basu nasara ba. Gwamnan ya bayyana hakane a yayin ganawa da wasu magoya bayansa. Yace yaji ance mataimakin nasa ya sauka daga mukaminsa amma har yanzu shi bai ga takardar ajiye aikin nasa ba.