Monday, May 4
Shadow
Daga gayawa Sheikh Pantami cewa kujerar Gwamna ta mai girma, sanata ya kamata ya fara nema shikenan yayi Blocking dina

Daga gayawa Sheikh Pantami cewa kujerar Gwamna ta mai girma, sanata ya kamata ya fara nema shikenan yayi Blocking dina

Duk Labarai
Wani ya bayyana cewa ya baiwa Farfesa Hon. Sheikh Isa Ali Pantami shawarar cewa ba gwamna ya kamata ya fara nema ba, Sanata ya kamata ya fara nema. Yace daga gayawa Pantamin hakan sai yayi Block dinsa. https://twitter.com/i/status/2051008353350881584 A jiya ne dai Farfesa Isa Ali Pantami ya bayyana cewa bai yadda da dan takarar bai daya da aka tsayar dashi a matsayin dan takarar Gwamnan jihar Gombe ba a jam'iyyar APC. https://twitter.com/i/status/2051067363856986116
Ban amince da Dan takarar Gwamna da APC ta zaba ba a jihar Gombe>>Inji Pantami

Ban amince da Dan takarar Gwamna da APC ta zaba ba a jihar Gombe>>Inji Pantami

Duk Labarai
Sheikh Farfesa Isa Ali Pantami ya bayyana cewa bai yadda da dan takarar da Jam'iyyar APC ta zaba ba a jihar Gombe a matsayin dan takarar Gwamna ba. Pantami ya bayyana cewa nadi ne aka yi wanda ba'a tuntubi sauran 'yan takara irinsa ba kamin a yi hakan ba kamar yanda doka ta tanada. Malam yace dan haka masoyansa kada su tayar da fitina su shiryawa zaben fidda gwani. Yace ya baiwa lauyoyinsa umarnin shiryawa dan daukar matakin da ya dace.
Kalli Bidiyon: Ashe Alhassan Ado Doguwa Gwamna Abba ya taba shiyasa aka hanashi takarar kujerarsa a APC

Kalli Bidiyon: Ashe Alhassan Ado Doguwa Gwamna Abba ya taba shiyasa aka hanashi takarar kujerarsa a APC

Duk Labarai
A dazu ne rahotanni suka yi yawa musamman a kafafen sada zumunta cewa, Jam'iyyar APC a jihar Kano, ta hana Alhassan Ado Doguwa takarar kujerar majalisar wakilai. Lamarin ya zowa mutane da yawa da mamaki ganin cewa ya shafe shekara da shekaru yana rike da wannan kujerar. Saidai wani Bidiyo ya bayyana a kafafen sadarwa inda aka ji yana sukar gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf kan cewar da yayi Kullu Nafsin Zalikatul Maut. Doguwa yacw abin kunyane ga jihar Kano a ji Gwamnanta ya fadi irin wannan maganar yana dan musulmi. https://twitter.com/i/status/2050926399045660896 Da yawa sun alakanta cewa wannan magana da Alhassan Ado Doguwa yayi ce tasa aka hanashi tikitin tsayawa takarar majalisar wakilansa.
Da Duminsa: A yau Kwankwaso da Peter Obi zasu shigo jam’iyyar mu>>Inji Jam’iyyar NDC

Da Duminsa: A yau Kwankwaso da Peter Obi zasu shigo jam’iyyar mu>>Inji Jam’iyyar NDC

Duk Labarai
Jam'iyyar NDC ta bayyana cewa, a yau, Lahadi, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso da Peter Obi zasu shiga cikin jam'iyyar. Jam'iyyar ta sanar da hakane ga manema labarai kamar yanda shahararren dan jarida daga gidan talabijin na Arise TV, Rufai Oseni ya sanar. Yace Duka Peter Obi da Kwankwaso zasu bar ADC su koma jam'iyyar NDC kamar yanda jami'iyyar ta NDC ta sanar dasu. Tuni dai Peter Obi ya sanar da ficewa daga jam'iyyar ADC.
Peter Obi ya fita daga jam’iyyar ADC

Peter Obi ya fita daga jam’iyyar ADC

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Peter Obi ya fice daga jam'iyyar ADC. Peter Obi ya bayyana hakanne a shafinsa na X. Yace abinda ya koroshi daga jam'iyyar Labour Party ne ya iske a jam'iyyar ADC shiyasa ya yanke shawarar fita daga cikinta Yace har yanzu yana girmama Atiku Abubakar da shugaban jam'iyyar, David Mark. Yace ba wai son neman takarar shugaban kasa ko ta mataimakin shugaban kasa ko ta kakakin majalisa ne yasa ya fice daga ADC ba. Yace ya ficene domin ganin an gyara Najeriya kowa yana jin dadi babu yunwa babu talauci.