Wannan wasu matan Musulmai ne da suka hadu a waje daya suke rokon Allah ya basu mazan aure.
Bidiyon nasu ya dauki hankula a kafafen sada zumunta.
https://twitter.com/i/status/2082136498930065823
'Yan Najeriya da yawa na ta zuwa yawon shakatawa a kofar Abuja bayan da Gwamnati ta gyarata.
An ga mutane na zuwa da masoya da abokai da iyalai anata daukar hotuna.
https://twitter.com/i/status/2082375171407511636
Likitan tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai, Abubakar Muhammad ya gayawa ICPC cewa shine ya bayar da takardar lafiya da ake takaddama akanta.
Likitan yace shine ya ya bayar da takardar amma bayanan dake kan takardar bana bogi bane.
ICPC ta yi zargin cewa bayanan dake kan takardar lafiyan na bogi ne kuma an yi hakanne dan a samu bayar da belin malam Nasiru Ahmad El-Rufai.
Saidai Likitan yace bayanan dake kan Takardar na gaskiya ne bai saba dokar aikinsa wajan bayar da takardar ba.
Yace kuma sun dade tare da malam Nasiru Ahmad El-Rufai tun shekarar 2005, yace ta hannnun matarsa suka san juna.
Wannan Wani Direban babbar motane da ya dauki hankula bayan da aka ganshi VIO sun tsayar dashi har sun hau kan motarshi amma yaki tsayawa.
An gansu sunata magana dashi amma yaki kulasu.
https://twitter.com/i/status/2082345402087416100
Wani Ango ya dauki hankula a kafafen sada zumunta bayan da yake ta danna wayarsa yaki kula amaryarsa a ranar aurensu.
Bidiyon ya jawo cece-kuce da muhawara a tsakanin masu amfani da kafafen sada zumunta
https://twitter.com/i/status/2082179280931369106
Wani ya sayi datar MTN ta naira 45,000 wadda suka ce Unlimited ce amma ta kare a cikin kwanaki 4 kacal.
Hakan yasa ya tafi ofishin MTN din inda ya musu korafi amma da alama dai bai yi nasarar samun warware matsalarsa ba.
https://twitter.com/i/status/2082345402087416100
Wasu dalibai a jami'ar Federal University Dutse dake jihar Jigawa sun tarawa malaminsu Sha tara ta arziki inda suka bashi kayan abinci da lemuka da sauransu.
Da yawa dai sun bayyana cewa duk yanda aka yi malamin na da kirki baya takura musu ne shiyasa suka masa haka.
https://www.tiktok.com/@fud_aeb_faces/video/7667581364681706772?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7667581364681706772&source=h5_m×tamp=1785314894&user_id=7483197776647635989&sec_user_id=MS4wLjABAAAAN7fVbcc0mzRzgIxdVwTekj-Bzgfq381B8aILPWs15fqP6aFNZ5GwIpbLEwMTYvVW&social_share_type=0&utm_source=copy&utm_campaign=client_share&utm_medium=android&share_iid=7665740753532061457&share_link_id=1aacaeea-739a-4...
Rufai Hanga na jam'iyyar NDC ya fasa Kwai cewa, Kwankwaso dansa, Mustapha yaso tsayarwa takarar gwamnan jihar Kano a jam'iyyar.
Ya bayyana hakane a wata hira da aka yi dashi a wani gidan radiyon Kano, kamar yanda jaridar Daily post ta ruwaito.
Hanga yace Kwankwaso ya aika masa da tawaga bisa jagorancin shugaban jam'iyyar NDC a jihar Kano, Hussaini Isa Mairiga inda ya shaida masa cewa, yana son tsayar da dansa, Mustapha a matsayin dan takarar Gwamna a jam'iyyar NDC.
Hanga yace ya musu fatan Alheri kuma yace a gayawa Kwankwaso a shirye yake ya zama manajan yakin neman zaben Dan Kwankwason.
Yace bai kara ji daga wajansu ba, sai daga baya Aminu Abdussalam ya sameshi yace masa Kwankwaso ya bashi takarar Gwamna kuma yana son ya zama mataimakinsa.
Hanga yace duk da yasan cewa muk...
A yayin da dukkan alamu suka nuna cewa Sanata Rufai Hanga ya kammala shiri tsaf dan komawa jam'iyyar APC, har ma aka ga wasu rahotanni na cewa ya ma riga ya koma APC.
A yanzu ya fito yace bashi da shirin barin jam'iyyar NDC ya koma APC.
Sanata Rufai Hanga ya bayyana hakane a wata hira da aka yi dashi a wani gidan Rediyo na Kano.
Hakan na zuwane bayan da aka ganshi ya gana da jiga-jigan jam'iyyar APC ciki hadda shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu.
Rufai Hanga yace Jam'iyyar su ta NDC ba zata ci zaben shugaban kasa ba amma zata ci Kano.
Da yake magana kan alakarsa da Kwankwaso yace tana nan kuma har yanzu suna girmama juna.
Tauraron Tiktok daga jamhuriyar Nijar, Hassan Make-Up ya bayyana cewa, Shafa Wali ta kirashi tace ya hakura ya daina fada da Sadiya Haruna.
Yace ya ji ya daina amma idan Sadiya ta sake masa Bidiyon da safe da rana gaskiya sai ya rama.
Sannan yace wallahi da abinda Shafa Wali ta masa gara ace wanine ya rasu a gidansu.
https://www.tiktok.com/@officielhassanmakeup227/video/7667845958524210440?_r=1&_t=ZS-98Qr4MwZlbR
Saidai dakatar da wannan fada da Shafa Wali ta yi baiwa 'yan Tiktok da yawa dadi ba inda suke ta sukarta.
Amma a martaninta, tace duk wanda ya zageta ta barshi da Allah ita dai tasan fada bashi da amfani.