Friday, August 7
Shadow
Da Duminsa: An yi min kutse an kwashe min kudi a asusun bankina>>Inji Atiku Abubakar

Da Duminsa: An yi min kutse an kwashe min kudi a asusun bankina>>Inji Atiku Abubakar

Duk Labarai
Tsohon Mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya bayyana cewa, an masa kutse a asusun bankinsa an kwashe masa kudade. Ya bayyana hakane a wata sanarwa da ya fitar ta bakin magana da yawunsa Frank Shu'aibu. Atiku yace bayanan bankin nasa babu wanda ya san dasu amma sai gashi an kwashe masa kudade a ciki. Yace idan mutum kamarsa za'a iya mai haka to lallai akwai matsala.
Kalli Bidiyon: Wata matashiya da aka kama bisa zargin zuwa Asibitin Babura dake jihar Jigawa ta shachi Jariri sabuwar Haihuwa

Kalli Bidiyon: Wata matashiya da aka kama bisa zargin zuwa Asibitin Babura dake jihar Jigawa ta shachi Jariri sabuwar Haihuwa

Duk Labarai
Wannan wata matashiyace da aka kama bisa zargin zuwa Asibitin Babura jihar Jigawa dan satar Jariri. Tace daga Unguwar Kinkinau take a jihar Kaduna inda take ta rokon su rufa mata Asiri kada iyayenta su gani. Ta bayyana cewa wai yaran idan suka daukesu tallafi za'a basu https://twitter.com/i/status/2085621216040144943
Kalli Bidiyon: Yanda matasa a Kano suka dakawa mata da suka ce taron APC wawa, Rahotanni sun ce hadda Teema Cool babbar me goyon bayan Gwamnan Kano

Kalli Bidiyon: Yanda matasa a Kano suka dakawa mata da suka ce taron APC wawa, Rahotanni sun ce hadda Teema Cool babbar me goyon bayan Gwamnan Kano

Duk Labarai
Bidiyo sun karade kafafen sada zumunta inda aka ga wasu mata da suka je taron jam'iyyar APC a Kano, dubban matasa sun daka musu wawa. A Bidiyon an ga matan zagaye da samari masu yawa. Waji Rahoton yace hadda Teema Cool wadda tana gaba-gaba wajan goyon bayan Gwamnatin Gwamnan Kano, Abba Gida-Gida. https://www.tiktok.com/@usersanikoki/video/7670981692068334856?_r=1&_t=ZS-98g05JH7QCA https://www.tiktok.com/@abdurrazak.ishak/video/7670984517611457799?_r=1&_t=ZS-98g1HcIBzLs https://www.tiktok.com/@teemahcool0/video/7671060799833574664?_r=1&_t=ZS-98g1h7Oj6lM Saidai ta fito ta karyata cewa itace. Rahotanni sun ce lamarin ya farune a Unguwar Kurna.
Kalli Bidiyon: Rikici ya barke tsakanin Rahama Saidu me babban Shago da yaran Shagonta inda ta zargesu da mata sata

Kalli Bidiyon: Rikici ya barke tsakanin Rahama Saidu me babban Shago da yaran Shagonta inda ta zargesu da mata sata

Duk Labarai
Rikici ya barke tsakanin Rahama Saidu me babban shago da yaran shagonta 3. Rahama Ta zargi yaran shagon da yi mata sata. Tace abaya 2 suka sace mata. Ta wallafa Sunayensu a shafinta na sada zumunta inda tace yanzu basa aiki da ita. A baya ta wallafa hadda hotuna da Bidiyon su kamar yanda suka yi zargi amma ta goge. Saidai daya daga cikin wadanda ta kora daga aikin, ta fito ta musanta wannan zargi. Tace abaya da tace sun bata sayarwa suka yi kuma an turawa Rahama kudinsu a asusun bankinta. Ta yi zargin cewa, Sun bayyana wa Rahama Saidu cewa ba zasu iya ci gaba da aiki da ita ba saboda albashin da take basu yayi kadan Shine ta fito da hanyar yi musu sharri. Ta kuma ce tana bin Rahama Saidu Albashin watanni 2 bata biyata ba. https://www.tiktok.com/@flowerbabyo1...
Magidanci a jihar Kaduna ya kai tsohuwar matarsa kotu saboda ta ki barin gidansa shekaru 2 bayan ya saketa

Magidanci a jihar Kaduna ya kai tsohuwar matarsa kotu saboda ta ki barin gidansa shekaru 2 bayan ya saketa

Duk Labarai
Wani magidanci a jihar Kaduna ya kai tsohuwar matarsa kotu saboda ta ki fita ta bar masa gida, Shekaru 2 bayan da ya saketa. Mutumin wanda dan kasuwane me suna Dauda Dahiru ya kai tsohuwar matartasa karane kotun magajin gari dake Kaduna. Da yake magana ta bakin lauyansa, Hassan Sadisu yace suna da 'ya'ya 5 mata da matar tasa da yaro namiji 1. Yace a lokacin da ya saketa tana dauke da cikinsa shine yace ta zauna sai ta haihu, yace amma ta haihu yanzu shekara 2 kenan da sakin amma taki fita daga gidan. Yace ya ma sayar da gidan sannan yace zai kama mata wani gidan saboda yara amma taki yadda. Matar dai a nata martanin tace idan yana son ta tashi sai ya sai mata gida ko da me daki dayane ko kuma ya kama mata haya ya biya kudin haya na shekaru 5. Saidai me shari'a, Mu’awiya...