Saturday, September 19
Shadow
Kalli Bidiyon: Matar Tsohon Shugaban kasa, Hajiya A’isha Buhari na shakatawa a kasar Spain

Kalli Bidiyon: Matar Tsohon Shugaban kasa, Hajiya A’isha Buhari na shakatawa a kasar Spain

Duk Labarai
Bidiyon matar tsohon shugaban kasa, Hajiya A'isha Buhari na shakatawa a kasar Spain ya dauki hankula. An ganta da kananan kaya suna shan Iska. A Bidiyon an nuna sauran manyan 'yan siyasar Najeriya irin su dan shugaban kasa, Seyi Tinubu da matarsa, Da sanata Dino Melaye da sauransu wanda suma suka je wannan waje dan shakatawa. Bidiyon ya jawo zazzafar Muhawara a tsakanin 'yan Najeriya. https://twitter.com/dammiedammie35/status/2101198825385849102
Rarara ya bayyana nawa aka bashi dan ya tallata Tinubu

Rarara ya bayyana nawa aka bashi dan ya tallata Tinubu

Duk Labarai
Dauda Kahutu Rarara ya bayyana nawa aka bashi dan ya tallata Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu. Ya bayyana hakanne a hira ta musamman da aka yi dashi a BBChausa. Yace lallai Shugaban yakin neman zaben shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu watau Sanata Abdulaziz Yari ya basu Naira Miliyan dari biyar Sannan kuma daga baya ya kara musu Naira Miliyan 50 yace su sha mai. https://twitter.com/bbchausa/status/2101167092980400593
Kalli Bidiyon: Samha M Inuwa ta bayyana cewa itama Babynta ya saya mata wayar iphone 18

Kalli Bidiyon: Samha M Inuwa ta bayyana cewa itama Babynta ya saya mata wayar iphone 18

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Hausa, Samha M Inuwa ta bayyana cewa, Itama babynta ya saya mata wayar iphone 18. Ta bayyana hakane a shafinta na sada zumunta inda ta wallafa Bidiyon wayar tana nunawa masoyanta. Wayar iPhone 18 dai farashinta yakan haura Naira Miliyan 4. https://www.tiktok.com/@samha_m_inuwa/video/7686931676030717204?_r=1&_t=ZN-99r6it04H3O
Kalli Bidiyon: Daya daga cikin masu hakar ma’adanai na jihar Naija ya bayyana cewa an fesa musu wani abu

Kalli Bidiyon: Daya daga cikin masu hakar ma’adanai na jihar Naija ya bayyana cewa an fesa musu wani abu

Duk Labarai
Daya daga cikin masu hakar ma'adanai na jihar Naija ya bayyana cewa bayan kamasu, inda aka sakasu a tsaye suka tsaya. Yace bayan nan an fesa musu wani abu me kama da Turare. Yace daga nan ne suka fita hayyacinsu. https://twitter.com/yabaleftonline/status/2100970601825354135 Ya bayyana hakane ga Ministan harkokin cikin gida Olubunmi Tunji-Ojo's a yayin da suke ganawa.
Kalli Bidiyon: Yanda ake dauki ba dadi tsakanin jami’an tsaro da jama’ar gari a jihar Naija kan abinda ya faru da masu hakar ma’adanai

Kalli Bidiyon: Yanda ake dauki ba dadi tsakanin jami’an tsaro da jama’ar gari a jihar Naija kan abinda ya faru da masu hakar ma’adanai

Duk Labarai
Biyo bayan matsalar da aka samu tsakanin masu hakar ma'adanai a jihar Naija. Jama'a sun fito zanga-zanga inda ake ta dauki ba dadi dasu da jami'an tsaro. https://twitter.com/NigeriaStories/status/2100902324654756274 Dalilin da yasa kenan ma Gwamnatin jihar Naija ta saka dokar hana zirga-zirga.
Kalli Bidiyon: OGAbba dake Ingila a yanzu yawa Gfresh Al-amin tallar wata Baturiya yace masa zai kawo mai ita Najeriya,Saidai Gfresh yace baya so

Kalli Bidiyon: OGAbba dake Ingila a yanzu yawa Gfresh Al-amin tallar wata Baturiya yace masa zai kawo mai ita Najeriya,Saidai Gfresh yace baya so

Duk Labarai
Mawakin Arewa, OGAbba da a yanzu haka yake a Landan kasar ingila yawa Gfresh Al-amin Tallar wata baturiya inda yace mai ko ya kawo mai ita Najeriya? Saidai Gfreh yace baya so, watau sai da ya gaji da ita sannan zai kawo mai ita? Saidai OGAbba yace ba Budurwarsa bace, Abokiyace. https://www.tiktok.com/@gfreshfanpage/video/7685875312671886599?_r=1&_t=ZN-99pZgDQc7HC
Daya daga cikin masu hakar ma’adanai a jihar Naija ya bayar da labarin yanda abokan sana’arsa suka rasa rayukansu

Daya daga cikin masu hakar ma’adanai a jihar Naija ya bayar da labarin yanda abokan sana’arsa suka rasa rayukansu

Duk Labarai
A yayin da rahotanni suka tabbatar da cewa mutane da dama sun rigamu gidan gaskiya a hannun Hukumomin Tsaro na NSCDC a jihar Naija. Daya daga cikin matasa masu hakar ma'adanai wanda ya tsira ya bayar da labarin yanda lamarin ya faru. Jami'an NSCDC sun kama Matasan da ake zargin da hakar ma'adanai ba bisa ka'idaba inda aka kaisu aka tsare wanda a inda ake tsare dasu ne rai yayi halinsa. Tuni dai aka dakatar da kwamandan Hukumar NSCDC na yankin inda aka fara gudanar da bincike. https://www.tiktok.com/@nuruddeendaza/video/7686534490512198932?_r=1&_t=ZN-99pWy6zDAog