Wednesday, April 22
Shadow
Farashin Dala a kasuwar Chanji ta yau

Farashin Dala a kasuwar Chanji ta yau

Duk Labarai
Farashin dala a kasuwar Chanji ta Gwamnati a yau, Laraba, 22 ga watan Afrilu ya kai Naira 1,348.77 NGN akan kowace dala. Farashin ya dan sauka zuwa Naira 1,346.30 NGN kamin daga baya ya sakw hawa. A kasuwar bayan fage kuwa ta garuruwan Abuja, Legas da Kano, Farashin dalar ya kai Naira 1,450 NGN zuwa naira 1,470 NGN akan kowace dala.
Kalli Bidiyon: Hudubar Adam A. Zango ta yi aiki a kaina, daga yau na daina nuna matata a kafafen sada zumunta>>Inji Gfresh Al-amin bayan daya kalli sabon fim din Adam A. Zango

Kalli Bidiyon: Hudubar Adam A. Zango ta yi aiki a kaina, daga yau na daina nuna matata a kafafen sada zumunta>>Inji Gfresh Al-amin bayan daya kalli sabon fim din Adam A. Zango

Duk Labarai
Tauraron Tiktok, Gfresh Al-amin yace Hudubar Adam A. Zango ta yi aiki akansa inda yace shima daga yau ya daina tallar matarsa a kafafen sada zumunta. Yace duka abokansa na da mata amma babu wanda yake ganin matansa sai shi sakarai ake ganin matarsa. Yace ya hau shafinta na Tiktok ya goge Bidiyon data dora sannan wanda take friends dasu ma ya gogesu. https://www.tiktok.com/@gfreshfanpage/video/7631339680214076680?_r=1&_t=ZS-95kERbNKtg9
Kalli Bidiyon: Gwamnati ta fara bin gidaje masu Amfani da Sola tana bukatar a biya Harajin Amfani da sola

Kalli Bidiyon: Gwamnati ta fara bin gidaje masu Amfani da Sola tana bukatar a biya Harajin Amfani da sola

Duk Labarai
A yayin da matsalar rashin wutar Lantarki ta damu Al'ummar Najeriya, suka koma amfani da Solar. Wani sabon salo shine da aka ga jami'an gwamnati sun fara bi gidaje dake amfani da Solar suna cewa, a basu harajin Amfani da Solar. Lamarin ya fara a Legas ne inda wani Magidanci yace ba zai biya ba bayan da aka rutsashi aka ce wai sai ya biya Harajin saka Solar. Bidiyon faruwar lamarin ya karade kafafen sadarwa inda ake ta cece-kuce akai. https://twitter.com/i/status/2046706370271981996
Mun Rabu da matatane saboda ita kullun take son a rika yi kuma sau biyu ya mata kadan>>Inji Roby Ekpo

Mun Rabu da matatane saboda ita kullun take son a rika yi kuma sau biyu ya mata kadan>>Inji Roby Ekpo

Duk Labarai
Shahararren ma'aikacin gidan rediyo daga kudancin Najeriya,Roby Ekpo ya bayyana cewa dalilin da yasa suka rabu da matarsa shine baya iya biya mata bukatar aure. Yace shi ba yaro bane, yayi aure yana da shekaru 37. Yace matarsa amma kullun take son su rika kwanciyar aure. Yace amma shi ba zai iya ba inda yace saidai sau biyu a sati amma taki amincewa da hakan. Yace dole saidai rabuwa suka yi
Kalli Bidiyon: Ashe Ministan Kudi, Wale Edun, Karyata shugaba Tinubu yayi shiyasa aka saukeshi

Kalli Bidiyon: Ashe Ministan Kudi, Wale Edun, Karyata shugaba Tinubu yayi shiyasa aka saukeshi

Duk Labarai
A dazune dai hutudole ya kawo muku rahoton cewa, Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya sauke ministan kudi, Wale Edun daga mukaminsa. Gwamnati dai bata bayyana dalilin sauke shi daga mukamin nasa ba a hukumance. Lamarin ya zowa mutane da mamaki duk da yake cewa a kwanakin baya an yi ta rade-radin cewa, Ministan yayi fama da rashin lafiya. Saidai a yanzu a kafafen sada zumunta, ana ta yada wani Bidiyo daya nuna shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu yana cewa sun cimma yawan kudin shiga da suke nema a shekarar 2025. Saidai a wani Bidiyo daban kuma, an ga Ministan kudin, Wale Edun na cewa Tiriliyan 40 suke nema a shekarar 2025 amma kudin shiga Tiriliyan 10 kacal suke tsammani. Wannan magana ta ci karo data shugaban kasa, wadda wannan yasa wasu ke ta hasashen cewa, dalili kenan da yasa...
Da Duminsa: Shugaba Tinubu ya sauke Ministan Kudi da Ministan gidaje

Da Duminsa: Shugaba Tinubu ya sauke Ministan Kudi da Ministan gidaje

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya sauke Ministan Kudi, Wale Edun da Ministan Gidaje Da ci gaban birane Umar Dangiwa. Sakataren Gwamnati, Sanata George Akume ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar. An baiwa Wale Edun umarnin ya mikawa karamin Ministan kudi, Mr. Taiwo Oyedele ragamar ma'aikatar. Hakanan shugaba Tinubu ya nada Mr. Muttaqha Rabe Darma (PhD) a matsayin Ministan Gidaje da ci gaban birane.
Kalli Bidiyon: A yaune Nafiu Bala Gombe ke gudanar da baban taron Jam’iyyar ADC tsagin da yake shugabanta amma babu kowa a wajan

Kalli Bidiyon: A yaune Nafiu Bala Gombe ke gudanar da baban taron Jam’iyyar ADC tsagin da yake shugabanta amma babu kowa a wajan

Duk Labarai
Rahotanni sun ce a yaune Nafiu Bala Gombe yake gudanar da babban taron jam'iyyar ADC tsaginsa inda zasu zabi shuwagabannin jam'iyyar. Saidai Bidiyon dake ta yawo a kafafen sada zumunta aun nuna cewa babu kowa a wajan taron Wasu rahotanni sun ce har Naira Dubu hamsin ake baiwa duk wanda ya yadda zai je wajan taron amma duk da haka babkowa. https://twitter.com/i/status/2046526118052651202
Babbar Kotun jihar Kaduna ta sake daga sauraron bayar da belin Malam Nasiru Ahmad El-Rufai sai zuwa watan June

Babbar Kotun jihar Kaduna ta sake daga sauraron bayar da belin Malam Nasiru Ahmad El-Rufai sai zuwa watan June

Duk Labarai
Da alama dai Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ba zai samu damar halartar zaben fidda gwani na jam'iyyar ADC ba. Saboda Mai shari'a Darius Khobo na babbar kotun jihar Kaduna ya sake daga sauraron belinsa sai satin farko na wajan Yuni. ICPC na ci gaba da tsare malam Nasiru Ahmad El-Rufai inda ake zarginsa da almundahanar kudade da aikata ba daidai ba da mukamin da ya samu na Gwamna da sauransu. Jam'iyyar ADC dai ta tsayar da karshen watan Afrilu zuwa Mayu dan gudanar da zaben fidda gwani.