Wednesday, April 15
Shadow
Tattalin arzikin Najeriya zai samu habaka fiye daga kasashen Amurka, Ingila, da Jamus>>Inji Fadar shugaban kasa

Tattalin arzikin Najeriya zai samu habaka fiye daga kasashen Amurka, Ingila, da Jamus>>Inji Fadar shugaban kasa

Duk Labarai
Fadar shugaban kasa, ta bayyana cewa, Tattalin arzikin Najeriya zai samu habaka sosai fiye dana kasashe masu arziki irin su Amurka, Ingila, da Jamus. Me magana da yawun shugaban kasa, Daniel Bwala ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar ta shafinsa na X inda yake martani kan bayanan habakar tattalin arziki da kungiyar bayar da lamuni ta Duniya, IMF ta fitar. IMF tace Najeriya zata samu habakar tattalin arziki da maki 4.1 a shekarar 2026. Wannan maki yafi na kasar Amurka wanda IMF tace 2.3 ne sannan yafi na kasar Ingila wanda IMF tace 0.8 ne hakanan yafi na kasar Jamus wanda shima 0.8 ne. Daniel yace Gwamnatin Tinubu ba da wasa take ba.
Matsalar tsaron Arewa ta kai matsayin Yaqi>>inji Kungiyar Tuntuba ta Arewa

Matsalar tsaron Arewa ta kai matsayin Yaqi>>inji Kungiyar Tuntuba ta Arewa

Duk Labarai
Kungiyar tuntuba ta Arewa, ACF ta bayyana cewa, matsalar tsaron da ake fama da ita ta kai matsayin yaki. Kungiyar tace tana kira ga Gwamnati data karkatar ta hankalinta da ma dukkan wani abu daya shafi kudi dan ganin an magance wannan matsala. Kungiyar ta bayyana matsayar tane bayan zaman data yi. Zaman ya samu halartar Tsohon shugaban sojoji, Janar Tukur Yusuf, Da Tsohon shugaban 'yansanda, Muhammad Abubakar, da tsohon sakataren majalisar Dinkin Duniya, Tijjani Muhammad-Bande, da tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Mahmud Ahmad, da shugaban kungiyar, Bashir Dalhatu. Sun bayyana cewa matsalar tsaron na jefa musamman yankin Arewa cikin tawayar tattalin arziki da kuma daidaita iyalai da sauransu.
Da Duminsa: Bayan Nafiu Bala Gombe, Jam’iyyar ADC ta sake korar karin wasu mutane daga cikinta

Da Duminsa: Bayan Nafiu Bala Gombe, Jam’iyyar ADC ta sake korar karin wasu mutane daga cikinta

Duk Labarai
jam'iyyar ADC ta fitar da cikaken bayanin mutanen daga kora daga jam'iyyar inda ta bayyana cewa maciya amana ne kuma sunawa jam'iyyar zagon kasa. Jam'iyyar tace ta dauki wannan mataki ne a babban taronta na kasa data gudanar a Abuja, kamar yanda me magana da yawun jam'iyyar, Bolaji Abdullahi ya sanar. Wadanda aka kora din sune kamar haka, Hon. Leke Abejide, Nafiu Bala Gombe, Mr. Kingsley Temitope Ogga, Mr. Don Norman Obinna, Mr. Kennedy Odion, Mr. Clement Ehigiator, Mrs. Stella Chukwuma, Patrick Ambut, Johny Tovie Derek, Duke Dick, and Elias Adikwu.
Me ya Faru? Malam Nasiru Ahmad El-Rufai zai ci gaba da zama a hannun ICPC duk da kotu ta bayar da belinsa

Me ya Faru? Malam Nasiru Ahmad El-Rufai zai ci gaba da zama a hannun ICPC duk da kotu ta bayar da belinsa

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, tsohon Gwamnan kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai zai ci gaba da zama a hannun hukumar ICPC duk da cewa kotu ta bayar da belinsa. Mai shari'a na babbar kotun tarayya dake Kaduna, Justice Rilwanu Aikawa ne ya bayar da belin malam Nasiru Ahmad El-Rufai a ranar Talata. Bayan bayar da belin nasa, El-Rufai yaki yin magana da manema labarai amma wani na kusa dashi ya shaidawa jaridar Daily Trust cewa, kotu ta saka sharuda 10 akan belin na Malam Nasiru Ahmad El-Rufai. Yace sai an cika wadannan sharudanne sannan za'a sakeshi.
Farashin dala a kasuwar Chanji a yau, Laraba

Farashin dala a kasuwar Chanji a yau, Laraba

Duk Labarai
Farashin dala a kasuwar Chanji ta Gwamnati a yau, Laraba 15 ga watan Afrilu ya fara ne akan Naira N1,352.25 kowace dala. Farashin ya dan tashi zuwa Naira N1,352.50 kamin daga baya ya koma ya daidaitu a farashin sama. A kasuwar bayan fage kuwa ta Kano, Abuja, da Lagos, Farashin dalar yana akan Naira N1,460 ne zuwa Naira N1,485 akan kowace dala.
Shugaban Amurka, Donald Trump na shirin daukar mataki dan baiwa Kiristocin Najeriya kariya

Shugaban Amurka, Donald Trump na shirin daukar mataki dan baiwa Kiristocin Najeriya kariya

Duk Labarai
Wasu majiyoyi daga kafar The Blaze sun bayyana cewa, Shugaban kasar Amurka, Donald Trump na shirij daukar wani sabon mataki dan baiwa Kiristocin Najeriya kariya. Rahoton yace, shugaba Trump na shirin daukar matakinne a asirce ba kamar a baya ba yanda ya rika yayatawa ba. Rahoton yace shugaban Amurka, Donald Trump ya fahimci cewa Najeriya na da muhimmanci sosai a nahiyar Afrika kuma duk wanda ya mallaketa ko ya iya juya akalarta, Kamar yana juya akalar gaba dayan Nahiyar Afrika ne. Dan hakane hankalinsa ya koma kan Najeriya. Najeriya tana daga cikin manyan kasashe 5 na kungiyar kasashen dake fitar da danyen man fetur, watau, OPEC, sannan tana da ma'adanan kasa da suka haura dala Tiriliyan wanda ba'a ma fara fito dasu ba.
Kalli Bidiyon yanda mutanen jihar Kwara suka ki karbar Tallafin shugaba Tinubu, Sun ce ba shine matsalarsu ba

Kalli Bidiyon yanda mutanen jihar Kwara suka ki karbar Tallafin shugaba Tinubu, Sun ce ba shine matsalarsu ba

Duk Labarai
Mutanen jihar Kwara sun ki karbar tallafin da aka kai musu na gwamnatin tarayya, karkashin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu. A wani Bidiyo da ya rika yawo a kafafen sada zumunta, an ga mutanen na jihar Kwara na cewa basa son tallafin kowa yaki karba. Jihar Kwara dai na daga cikin jihohin dake fama da matsalar tsaro sosai. A baya ma, Jihar Benue sun fito sun ce basa son tallafin shinkafa na Gwamnatin Tinubu inda suka ce ba shine matsalarsu ba. https://twitter.com/i/status/2043695469109313876
Da Duminsa: Rahotanni sun bayyana cewa, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai zai fito takarar shugaban kasa a 2027, yayi martani

Da Duminsa: Rahotanni sun bayyana cewa, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai zai fito takarar shugaban kasa a 2027, yayi martani

Duk Labarai
Wani na kusa da Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana cewa, El-Rufai zai tsaya takarar shugaban kasa. Rahotan ya watsu sosai a kafafen sada zumunta. Saidai a martaninsa ta bakin me magana da yawunsa, Muyiwa Adekeye, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana cewa, wannan Rahotan ba gaskiya bane. Yace wani ne na kusa dashi ya bayyana ra'ayinsa amma ba daga bakinsa maganar ta fito ba. Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya ce ba zai ji tsoron fitowa ya bayyana ra'ayinsa na siyasa ba idan yanaso.
Sai mutanen Arewa sun daina aure barkatai da haihuwar ‘ya’yan da basu iya kula dasu sannan matsalar tsaro zata zo karshe a Najeriya>> Inji Me magana da yawun Ministan Abuja

Sai mutanen Arewa sun daina aure barkatai da haihuwar ‘ya’yan da basu iya kula dasu sannan matsalar tsaro zata zo karshe a Najeriya>> Inji Me magana da yawun Ministan Abuja

Duk Labarai
Babban Hadimin ministan Abuja ta bangaren sadarwa, Lere Olayinka ya soki mutanen, Arewa inda yace yanayin tsarin rayuwarsu ta auren mata barkatai da haihuwar 'ya'yan da basu iya kulawa dasu ne ke kara rura wutar matsalar tsaron Yace ta yaya me gadi dake daukar Albashin dubu 60 zai auri mata 4 ya haifi 'ya'ya 17 ace ba za'a samu matsala ba? Yace gasunan a Abuja kullun suna ganinsu da robar bara idan ya gansu yakan yi tunanin shin nan gaba wane irin mutane wadannan yaran zasu zama? Yace wasu zasu zargi Gwamnati amma maganar gaskiya wannan ba laifin Gwamnati bane.