Friday, February 27
Shadow
Kalli Bidiyon: Yanda wani dan kasuwar China ya bajewa ma’aikatansa kudi da suka kai dala Miliyan 26 akan teburi kowa ya kwashi iya abinda zai iya kwasa

Kalli Bidiyon: Yanda wani dan kasuwar China ya bajewa ma’aikatansa kudi da suka kai dala Miliyan 26 akan teburi kowa ya kwashi iya abinda zai iya kwasa

Duk Labarai
Wani dan kasuwar kasar China ya bajewa ma'aikatansa kudi da suka kai dala Miliyan $26 akan Teburi inda yace kowane ya kwashi abinda zai iya kwasa. Yace yayi hakan ne dan saukaka musu rayuwa saboda tsadar rayuwa ta yi yawa kuma wasu ana binsu bashi. Lamarin dai ya dauki hankula sosai inda ake ta yaba masa. https://twitter.com/i/status/2027141537751040502
Wata mata wadda tace ita ‘yar Kwangila ce, tace ta kaiwa Ministan Ayyuka, David Umahi kayan aiki na Naira Miliyan 304 Shekaru 12 da suka gabata amma yaki biyanta

Wata mata wadda tace ita ‘yar Kwangila ce, tace ta kaiwa Ministan Ayyuka, David Umahi kayan aiki na Naira Miliyan 304 Shekaru 12 da suka gabata amma yaki biyanta

Duk Labarai
Wata mata me suna Tracy Nicolas Ohiri ta bayyana inda ta zargi Ministan ayyuka, David Umahi da kin biyanta kudin kayan aiki data kai masa. Matar tace ta kaiwa Ministan kayan aiki na Naira Miliyan 304 tun shekaru 12 da suka gabata amma yaki biyanta kudin. A jawabin da takewa manema labarai ta zargi Ministan da neman ta su yi soyayya amma tace masa a'a domin ita matar aurece. Tace tana da chat din da suka yi da kum irin maganganun da ya rika gaya mata wanda basu dace ba. Matar dai ta fito ta gayawa Duniya inda hakan yasa aka tura 'yansanda su kamata daga legas zuwa Abuja aka tsareta https://twitter.com/i/status/2027019991048994903 Dan Fafutuka, Omoyele Sowore ya shiga lamarin inda a zaman da aka yi da matar da 'yansanda da David Umahi, Ministan yace be san matar ba inda t...
An yi Min wahayi cewa nan da shekarar 2027 wani shugaban kasa zai bar Duniya>>Inji Fasto Elijah Ayodele

An yi Min wahayi cewa nan da shekarar 2027 wani shugaban kasa zai bar Duniya>>Inji Fasto Elijah Ayodele

Duk Labarai
Fasto Elijah Ayodele wanda ya saba kawo maganganu masu jawo cece-kuce yace nan da shekarar 2027 wani shugaban kasa zai garzaya Barzahu. Ya bayyana hakane a wata sanarwa da ya fitar, saidai bai yi karin haske game a sanarwar ba domin bai fadi sunan shugaban kasar ba. A baya dai ya yi ta fadar irin wadannan abubuwan na hasashe inda yakan ce an masa wahayi.
Wani Abokin Tauraron mawakin Najeriya, Burna Boy ya kara tabbatar da cewa mawakin ya musulunta

Wani Abokin Tauraron mawakin Najeriya, Burna Boy ya kara tabbatar da cewa mawakin ya musulunta

Duk Labarai
Wani Abokin Burna Boy ya tabbatar da cewa ya musulunta. A baya dai an ta yada cewa, Burna Boy ya Musulunta, Inda aka ga Bidiyonsa yana fadar hakan. Saidai da yawa sun rika yin shakkar hakan. A yanzu na kusa da Burna Boy din me suna, Rahman Jago ya wallafa Bidiyon Burna Boy yana Zikiri ga Allah. Sannan ya kara tabbatar da cewa mawakin ya musulunta. https://twitter.com/i/status/2026816285846225387 https://twitter.com/i/status/2026877686023344446
Duk Kannywood babu wanda yafi karfin shinkafa>>Inji Garzali Miko

Duk Kannywood babu wanda yafi karfin shinkafa>>Inji Garzali Miko

Duk Labarai
Tauraron Kannywood, Garzali Miko ya halarci gidan abokin aikinsa, Nuhu Abdullahi inda sua yi shan ruwa acan. An ji yana jinjinawa Nuhu yana fadar cewa, gashi ga me kudi. https://www.tiktok.com/@garzalimiko/video/7610895597519785237?_r=1&_t=ZS-94F5Em9fboO https://www.tiktok.com/@kb_international/video/7610527513944591623?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7610527513944591623&source=h5_m&timestamp=1772111994&user_id=7483197776647635989&sec_user_id=MS4wLjABAAAAN7fVbcc0mzRzgIxdVwTekj-Bzgfq381B8aILPWs15fqP6aFNZ5GwIpbLEwMTYvVW&item_author_type=2&social_share_type=0&utm_source=copy&utm_campaign=client_share&utm_medium=android&share_iid=7606977366144993025&share_...
Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un: Ji abinda wasu da ba musulmai ba suka yi a babban masallacin Manchester dake kasar Ingila ana tsaka da sallar Tarawihi

Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un: Ji abinda wasu da ba musulmai ba suka yi a babban masallacin Manchester dake kasar Ingila ana tsaka da sallar Tarawihi

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa a ranar 24 ga watan Fabrairu, wasu mutane 2 wanda ba musulmai ba sun shiga babban masallacin Manchester dake kasar Ingila yayin da ake tsaka da sallar Tarawih. Masallatan sun kama daya da wasu maqamay a hannunsa an bayyana mutumin a matsayin dan kimanin shekaru 40 inda kuma dayan ya tsere har yanzu ana nemansa. Babu dai rahoton cewa, wani ya jikkata ko rasa rai. Firaiministan Ingila, Keir Stermer yayi Allah wadai da lamarin inda ya jinjinawa wadanda suka kama daya daga cikin masu laifin. Ya bayyana cewa sun ware kudi har fan Miliyan £40 dan samar da karin tsaro a masallatai da makarantun Islamiya, da kuma yankunan da musulmai suke. Rahotanni sun ce masallacin ya dauki matakan tsaro dan kiyaye kara faruwar hakan https://twitter.com/i/status/...
Allah Sarki Kalli Bidiyon: Yanda wani Mahaifi dake aikin hakar ma’adanai ya tara kudi ya saiwa ‘ya’yansa Talabijin(TV) da suka dade suna son ya sai musu

Allah Sarki Kalli Bidiyon: Yanda wani Mahaifi dake aikin hakar ma’adanai ya tara kudi ya saiwa ‘ya’yansa Talabijin(TV) da suka dade suna son ya sai musu

Duk Labarai
Wannan wani mahaifine da ke aiki a wajan hakan ma'adanai da ya tara kudi ya saiwa 'ya'yansa Talabijin(TV) da suka dade auna son ya sai musu. A nan ya sai musu talabijin dinne, kuma yanda suka saki baki suna kallo shine ya dauki Bidiyonsu ya watsawa Duniya. Da yawa sun jinjina masa. https://twitter.com/i/status/2026424085127823521