Sunday, April 19
Shadow
Kalli Bidiyon: Malami ya bayyana abin mamakin da ya gani a ajin da ya je koyar da dalibai a jami’ar Federal University Kashere, Jihar Gombe

Kalli Bidiyon: Malami ya bayyana abin mamakin da ya gani a ajin da ya je koyar da dalibai a jami’ar Federal University Kashere, Jihar Gombe

Duk Labarai
Wani malami da ya je koyar da dalibai a jami'ar Federal University Kashere dake jihar Gombe ya bayyana cewa ya je ya iske ajin ba kowa. Ya dauki Bidiyon ajin inda aka ga kujeru inda yace zai koma ofis ya tafi gida. https://www.tiktok.com/@amedkt1/video/7630389740956634389?_r=1&_t=ZS-95gGL3UR7Wz
Da Duminsa: Gwamnatin tarayya ta dauki bashin Naira Biliyan 100 a asusun bankunan ‘yan Najeriya

Da Duminsa: Gwamnatin tarayya ta dauki bashin Naira Biliyan 100 a asusun bankunan ‘yan Najeriya

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Gwamnatin tarayya ta karbi bashin Naira Biliyan 100 daga asusun bankunan 'yan Najeriya wadanda ba'a amfani dasu, wanda a turance ake kira da Dormant account. Hakanan ta dauki kudaden daga ribar kamfanoni wadda mutane masu hannun jari a kamfanonin basu karbaba wadda a turance ake kira da Dividend. Wata dokar kudi da aka yi a shekarar 2020 ce ta baiwa Gwamnatin tarayya damar rantar irin wadannan kudade.
Kuma Dai: Sheikh Farfesa Isa Ali Pantami ya sake yin Blocking wata data tambayeshi dan Allah ya bata Miliyan 2 ta ja jari

Kuma Dai: Sheikh Farfesa Isa Ali Pantami ya sake yin Blocking wata data tambayeshi dan Allah ya bata Miliyan 2 ta ja jari

Duk Labarai
A dazu ne dai muka di wani Dr. Adam ya koka cewa dan takarar Gwamnan jihar Gombe, Farfesa Ali Pantami ya yi Blocking dinsa saboda ya gaya masa gaskiya a cewar Adamu A yanzu kuwa watace itama me suna Huraira ta roki mallam ya bata Miliyan 2 ta ja jari bayan ta ganshi a jirgin sama. Saidai itama yayi Blocking dinta. A karshe dai ta roki malam ko dubu dari biyu ya bata. https://twitter.com/i/status/2045896467609420011
Da Duminsa: Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana wata maqarqashiya da ake shirya masa dan ci gaba da tsereshi

Da Duminsa: Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana wata maqarqashiya da ake shirya masa dan ci gaba da tsereshi

Duk Labarai
Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana wata Mqarqashiya da yace ana shirya masa dan ci haba da tsareshi na tsawon lokaci. Ya bayyana hakane ta bakin me magana da yawunsa, Muyiwa Adekeye inda yace Jaridar The Nation ta ruwaito cewa, wai daya daga cikin masu bayar da shaida akansa me suna Mohammed Umar Karage 'yan Bindiga sun shiga gidansa. Ya zargi cewa harin da aka kai masa bai rasa nasaba da shaidar da yake bayarwa akan malam Nasiru Ahmad El-Rufai. Dan hakane Malam Nasiru Ahmad El-Rufai yace wannan bata sunane kuma ya baiwa lauyoyinsa umarnin su kai karar gidan jaridar. Ya bayyana cewa bashi da hannun a harin da aka kaiwa shaidar nasa dan shi mutum ne me son bin doka da oda.
Daga gayawa Sheikh Pantamu gaskiya a Shafin sada zumunta sai ya yi Blocking dina>>Inji Dr. Adam Umar

Daga gayawa Sheikh Pantamu gaskiya a Shafin sada zumunta sai ya yi Blocking dina>>Inji Dr. Adam Umar

Duk Labarai
Me amfani da kafafen sada zumunta, Dr. Adam Umar ya bayyana cewa, daga ya gayawa farfesa Isa Ali Pantami Gaskiya kawai sai ya yi Blocking dinsa. Ya bayyana hakane a shafinsa na X Ya ga wani Bidiyon Sheikh Pantami a jirgin sama ne shine ya rubuta masa: "hmmm Allah sarki duniya. Duk abubuwan yan siyasa din da kakeyin hani da shi kayi. Private jet shatter the cheapest fare is 10,000$ (abt 14million), a journey that u can do with just about 300k naira. Even if it was paid for u, the mallam we know in the past could reject it bt hmm" https://twitter.com/i/status/2045367705113383111 Saidai yace bayan Hakan, Pantami yayi Block dinsa https://twitter.com/i/status/2045494899953283400 Yace abinnya matukar bashi mamaki.
Kalli Bidiyon: Bana kewar gidan Sani Danja kuma bazan taba komawa ba>>Inji Mansurah Isah

Kalli Bidiyon: Bana kewar gidan Sani Danja kuma bazan taba komawa ba>>Inji Mansurah Isah

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Hausa, Mansurah Isah ta bayyana cewa, bata kewar gidan tsohon mijinta, Kuma abokin aikinta, Sani Musa Danja. Mansurah tace kuma ba ta da shirin komawa gidan tsohon mijin nata. https://www.tiktok.com/@madina.bbc.hausa/video/7629826012397784338?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7629826012397784338&source=h5_m&timestamp=1776512399&user_id=7483197776647635989&sec_user_id=MS4wLjABAAAAN7fVbcc0mzRzgIxdVwTekj-Bzgfq381B8aILPWs15fqP6aFNZ5GwIpbLEwMTYvVW&item_author_type=2&social_share_type=0&utm_source=copy&utm_campaign=client_share&utm_medium=android&share_iid=7625183675001341712&share_link_id=87a6d1ad-cfd1-463a-9ae4-6106b6cd29ec&share_app_id=1233&...