Thursday, May 22
Shadow
Kalli Bidiyo Gwanin ban Tausai: Yanda Mijina ya hanani zuwa jana’izar babana bayan ya ràsù, inji wannan matar

Kalli Bidiyo Gwanin ban Tausai: Yanda Mijina ya hanani zuwa jana’izar babana bayan ya ràsù, inji wannan matar

Duk Labarai
Wannan matar ta dauki hankula sosai a kafafen sadarwa bayan da ta yi zargin cewa, mijinta ya gallaza mata. Tace abinda ba zata taba mantawa dashi ba shine mahaifinta ya rasu amma ya hanata ta je jana'iza. Kalli Cikakkiyar hirar da aka yi dashi: https://www.tiktok.com/@bcrw.social.spotlight/video/7506277106347822392?_t=ZM-8wYy46Fya0c&_r=1 Labarin nata dai ya zowa mutane kamar Almara inda akai ta mamaki.
Kaso 85 na wadanda muke daukar nauyinsu mu aikasu karatu kasashen Turawa basa dawowa dan su taimaka a gina kasarnan>>Gwamnatin Tarayya ta koka

Kaso 85 na wadanda muke daukar nauyinsu mu aikasu karatu kasashen Turawa basa dawowa dan su taimaka a gina kasarnan>>Gwamnatin Tarayya ta koka

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya ta koka da cewa, Kaso 85 na daliban Najeriya da take daukar nauyinsu dan zuwa kasashen waje su karo ilimi da zummar su dawo dan ciyar da Najeriya gaba, basa dawowa. Ministan Ilimi, Dr Tunji Alausa ne ya bayyana hakan a wajan wani taro da ya wakana a Legas. Yace dalilin haka yasa suka canja lissafi domin sun gano cewa yawanci karatun da ake daukar nauyin daliban su je su yi a kasashen da suka ci gaba, za'a iya yinsa a Najeriya. Yace dan hakane suka mayar da hankali wajan karfafa harkar ilimin a Najeriya inda yace sun bude cibiyoyin bincike da zurfafa ilimi a jami'o'i daban-daban na kasarnan.
Jimullar masu laifi 2000 ne suka tsere daga gidajen yarin Najeriya kuma ake nema ruwa a jallo

Jimullar masu laifi 2000 ne suka tsere daga gidajen yarin Najeriya kuma ake nema ruwa a jallo

Duk Labarai
Bayan tserewar masu laifi daga gidan yarin Ilesa na jihar Osun su 7 ranar Talata, an gano cewa akwai masu laifi 2000 da suka tsere daga gidajen yari daban-daban na Najeriya da ake nema ruwa a jallo. Haka na zuwane wata daya kacal bayan da masu laifi 12 daga gidan yari me suna Katon Karfe suka tsere daga jihar Kogi. A shekarar 2024 ma dai an samu tserewar masu laifi daga gidan yarin MCC dake Suleja jihar Naija inda masu laifi 118 suka tsere amma guda 23 ne kawai aka samu damar sake kamowa. Hakan na zuwane yayin da laifuka da kashe-kashen da ayyukan ta'addanci suka yi yawa a Najeriya. Rahoton yace zuwa yanzu akwai jimullar masu laifi 2000 da suka tsere daga gidajen yarin Najeriya daban-daban.
JAMB zata sakewa wadanda basu samu damar rubuta jarabawar ba

JAMB zata sakewa wadanda basu samu damar rubuta jarabawar ba

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Hukumar shirya jarabawar shiga jami'a ta JAMB zata sake shiryawa daliban da suka yi fashi basu samu damar rubuta jarabawar ba. Shugaban hukumar, ta JAMB Prof. Is-haq Oloyede ne ya bayyana haka a yayin ganawa da manema labarai a Abuja ranar Laraba. Yace hukumar zata shiryawa kaso 5.6 na daliban da basu samu damar rubuta jarabawar ba. An dai zargi JAMB din da saka lokaci wanda yayiwa dalibai wahalar iya zuwa wajan jarabawar akan kari.
Ta tabbata dai Hadaka me karfi tsakanin Atiku da Peter Obi ta kullu, APC ta kadu inda ta yi magana kan lamarin

Ta tabbata dai Hadaka me karfi tsakanin Atiku da Peter Obi ta kullu, APC ta kadu inda ta yi magana kan lamarin

Duk Labarai
Rahotanni na kara bayyana dake tabbatar da alaka me karfi tsakanin Atiku Abubakar da Peter Obi ta kullu. Rahotannin sun ce, duka bangarorin sun saka hannu a wata yarjejeniya da suka akince da ita. A tafiyar dai akwai tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai da Tsohon Ministan sufuri, Rotimi Amaechi da sauransu. Hakanan rahoton yace sun kuma amince da komawa jam'iyyar ADC da kuma saka kudi dan gyara jam'iyyar. Saidai duk da El-Rufai shi yana SDP ne, rahoton yace da zarar an kammala shirya komai, za'a sanar da kulla alaka tsakanin SDP da ADC din. A bangaren APC kuwa, sakataren jam'iyyar Ajibola Basiru ya bayyana cewa shugaban kasa Bola Tinubu shine uban hada kan al'umma kuma suna da yakinin shi zai lashe zaben shekarar 2027.
Da Duminsa: An kàshè ma’aikatan ofishin jakadancin Israeyla 2 a babban birnin kasar Amurka, Washington DC

Da Duminsa: An kàshè ma’aikatan ofishin jakadancin Israeyla 2 a babban birnin kasar Amurka, Washington DC

Duk Labarai
Rahotanni daga babban birnin kasar Amurka, Washington DC na cewa an kashe ma'aikatan ofishin jakadancin kasar Israela 2. An bayyana lamarin da cewa Kiyayya ce ga Yahudawa. Wani rahoto yace maharbin yayi ihun cewa a kyale Falasdinawa kamij ya kashe mutanen. Shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya bayyana Allah wadai da lamarin inda yace irin wannan lamari bashi da mazauni a kasarsu.
Gidajen Sayar da Man Fetur kusan Dubu biya sun kulle saboda rashin tabbas na farashi da yawaitar rage farashin da Dangote yake

Gidajen Sayar da Man Fetur kusan Dubu biya sun kulle saboda rashin tabbas na farashi da yawaitar rage farashin da Dangote yake

Duk Labarai
Rahotanni sun ce gidajen saye d man fetur akalla 4900 ne suka kulle a fadin kasarnan saboda rashin tabbas na kasuwar man fetur din. 'Yan kasuwar da yawa basa iya sayen tankar mai, inda a yanzu sai ka da an hada kudi na 'yan kasuwa biyu zuwa uku kamin su samu damar sayen tankar man fetur daya wadda a baya cikin sauki mutum daya ke iya sayenta. Daga watan Janairu na shekarar 2025 zuwa Afrilu matatar man fetur ta Dangote ta rage farashin ta sau 6 inda ya fara a Naira 950 har ya sakko zuwa 835. 'Yan kasuwar da basu ma da kudin da za'a yi wannan hadaka dasu dole tasa sun rufe gidajen man fetur din. Bayan zuwan Gwamnatin Bola Ahmad Tinubu, Ta cire tallafin man fetur wanda hakan yasa farashin ya koma hannun 'yan kasuwa.
Hotunan kananan yara da nake gani suna wahala a Gàzà akwai ban tausai, ina kira gareka da a kawo karshen wannan yàkì>>Shugaban Amurka Donald Trump ya sake yiwa Benjamin Netanyahu magana

Hotunan kananan yara da nake gani suna wahala a Gàzà akwai ban tausai, ina kira gareka da a kawo karshen wannan yàkì>>Shugaban Amurka Donald Trump ya sake yiwa Benjamin Netanyahu magana

Duk Labarai
Rahotanni daga fadar shugaban kasar Amurka, White House na cewa, shugaban Amurka, Donald Trump ya sake yin kira ga Firaiministan Israyla Benjamin Netanyahu da a kawo karshen yakin da suke yi da kungiyar Hàmàs. Trump yace ya damu da hotunan da ya gani na yara suna shan wahala a Gaza yace abin akwai ban tausai. Yace a yi sulhu sannan a saki wadanda aka yi garkuwa dasu sannan a kawo karshen yakin. Jaridar Axios ta kasar Amurka tace wasu majiyoyi biyu sun shaida mata hakan daga fadar ta White House.
Daya daga cikin masu laifin da suka tsere daga gidan yari yace a aikawa mahaifiyarsa Ladar Naira Miliyan 5 da aka saka ga duk wanda ya taimaka aka kamasu shi kuma zai koma gidan yarin da kanshi

Daya daga cikin masu laifin da suka tsere daga gidan yari yace a aikawa mahaifiyarsa Ladar Naira Miliyan 5 da aka saka ga duk wanda ya taimaka aka kamasu shi kuma zai koma gidan yarin da kanshi

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Gwamnati ta saka ladar Naira Miliyan 5 ga duk wanda ya taimaka aka kama wadanda suka tsere daga gidan yarin Ilesa na jihar Osun. Saidai wani shafi a Twitter wanda yake ikirarin shi daya daga cikin wadanda ake nema ne yace damfarar dala $20 kawai yayi aka kamashi. Yace amma a aikawa Mahaifiyarsa Miliyan 5 din da aka ce an saka akan duk wanda ya taimaka aka kamasu shi kuma zai koma gidan yarin da kansa. https://twitter.com/illxgally/status/1925263845938852073?t=W7WZEzT9q4WDx1QjtJ9pLg&s=19 Saidai wasu na shakkun cewa ba shi bane.