Tuesday, March 31
Shadow
ICPC ta sake kama Malam Nasiru Ahmad El-Rufai bayan zaman kotun yau

ICPC ta sake kama Malam Nasiru Ahmad El-Rufai bayan zaman kotun yau

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Hukumar ICPC ta sake kama tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai a yau bayan zaman kotun da aka yi. Malam Nasiru Ahmad El-Rufai dai ya nemi beli inda kotu ta saka ranar Laraba, 1 ga watan Afrilu dan yanke hukunci. A baya dai ICPC sun ce sun saki malam Nasiru Ahmad El-Rufai ne saboda tausayi bayan rasuwar mahaifiyarsa inda ya samu halartar jana'izar da aka mata. https://twitter.com/i/status/2038967971477962970
Da Duminsa:  Rahotanni na cewa, wasu matasa sun yiwa Musa Mai Sana’a na jaki

Da Duminsa: Rahotanni na cewa, wasu matasa sun yiwa Musa Mai Sana’a na jaki

Duk Labarai
Rahotanni na ta yawo a kafafen sada zumunta inda ake yada cewa wasu matasa sun tare Tauraron fina-finan Hausa, Musa Mai Sana'a inda suka masa na jaki. Shafin @kafinhausa dake X ya wallafa cewa, lamarin ya farune a Sharada dake Kano. Mai Sana'a dai bai tabbatar da hakan da kansa ba, sannan babu wata kafa data kawo labarin, saidai labarin ya dauki hankula a kafafen sada zumunta inda mutane ke ta bayyana ra'ayoyinsu akai. https://twitter.com/i/status/2038737606788149299

Da Duminsa: Bayanin Halin da ake ciki a kotun da aka mayar da Malam Nasiru Ahmad El-Rufai a yau

Duk Labarai
A yaune dai ICPC ta mayar da Malam Nasiru Ahmad El-Rufai babbar kotun jihar inda ake masa shari'a game da zargin Almundahanar kudade. Saidai kotun tace zaman kotun ba zai yiyu ba saboda dayan wanda ake musu shari'ar tare da malam Nasiru Ahmad El-Rufai bai zo ba saboda bai da lafiya kuma shari'ar ta mutum biyu ce dan haka ba zai yiyu a ci gaba da ita ba sai yana nan. A yanzu za'a tafi da malam Nasiru Ahmad El-Rufai zuwa babbar kotun tarayya inda za'a saurari neman belin da yayi. KARIN BAYANI: An kuma je babbar kotun tarayya inda El-Rufai ya shigar da korafin neman beli, saidai an daga ci gaba da sauraren karar har sai nan da 1 ga watan Afrilu
Dubban Mutane sun kamu da cutar Kanjamau daga wajan Janairu na shekarar 2026 zuwa yanzu

Dubban Mutane sun kamu da cutar Kanjamau daga wajan Janairu na shekarar 2026 zuwa yanzu

Duk Labarai
Sabbin alkaluma sun nuna cewa, dubban mutanene suka kamu da cuta me karya garkuwar jiki, wadda aka fi sani da Kanjamau a Najeriya. An fitar da yawan mutanen da suka kami a kowace jiha, yayin da a Arewa, Jihar Kaduna ce kan gama da yawan mutane 800 da suka kami da cutar. Yayin da jihar Yobe itace ta karshe inda mutane 100 ne kacal auka kamu da cutar a wannan tsakani. Numbers of newly tested HIV positive patients in Nigeria (Jan-Mar, 2026) Lagos: 2,298 ⁠Benue: 1,949 ⁠Akwa Ibom: 1,159 ⁠Rivers: 1,137 ⁠Anambra: 1,013 ⁠Kaduna: 842 ⁠Delta: 803 ⁠Oyo: 763 ⁠Ogun: 751 ⁠Plateau: 662 ⁠Imo: 640 ⁠Nasarawa: 615 ⁠Taraba: 605 ⁠FCT: 579 ⁠Abia: 527 ⁠Edo: 512 ⁠Enugu: 479 ⁠Kano: 476 ⁠Kogi: 422 ⁠Cross River: 396 ⁠Niger: 387 ⁠Adamawa: 38...
Ashe Tsugune bata kare ba, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai  ya bayyana wata Mugunta da Gwamnati ta shirya masa dan tursasashi ya amince da bukatun Gwamnatin

Ashe Tsugune bata kare ba, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana wata Mugunta da Gwamnati ta shirya masa dan tursasashi ya amince da bukatun Gwamnatin

Duk Labarai
Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya yi zargin cewa, Gwamnati na son kama yayansa, Bashir El-Rufai dan a tursasashi ya amince da bukatun Gwamnatin. Yace dalili ma kenan da yasa suka ce babban yayan nasu ya tsaya a birnin Cairo na kasar Egypt kada ya dawo Najeriya dan kar a kamashi. Yace yanzu haka yana can. ElRufai ya bayyana hakane a wajan zaman makokin mahaifiyar sa data rasu inda yakewa mutane godiya da irin aoyayyar da suka nuna musu. https://twitter.com/i/status/2038828878110626286
Farashin dala a kasuwar Chanji ayau, Talata

Farashin dala a kasuwar Chanji ayau, Talata

Duk Labarai
Farashin Dala a kasuwar chanji ta Gwamnati a yau Talata, 31 ga watan Maris na shekarar 2026 ya farane akan Naira ₦1,385.60 kowace dala. Saidai da gari ya kara wayewa, farashin ya sauka zuwa Naira ₦1,383.37 akan kowace dala. A kasuwar bayan fage ta Legas da Abuja kuwa farashin dalar yana akan naira ₦1,405 zuwa Naira ₦1,420 akan kowace dala daya.
Kalli Bidiyon: Tauraron dake fadakarwa a Tiktok, Dr. Hussain Kano ya bayyana cewa yana son Tauraruwar mawakiya, Fati Nijar da aure

Kalli Bidiyon: Tauraron dake fadakarwa a Tiktok, Dr. Hussain Kano ya bayyana cewa yana son Tauraruwar mawakiya, Fati Nijar da aure

Duk Labarai
Tauraron dake fadakarwa a kafafen sadarwa, Dr. Hussain Kano ya bayyana cewa, yana son Tauraruwar mawakiyar Hausa, Fati Nijar Ya bayyana hakane a wani Bidiyo daya wallafa inda yace indai tana sonsa, to shima yana sonta. Yace tuni ya aika mata sakon soyayya kuma yana jiran amsarta. https://www.tiktok.com/@dr.hussainkano5/video/7622380031565729031?_r=1&_t=ZS-958CXOwUaMj&sp_source=7537614245375297080
Ta bayyana a fili cewa, Gwamnatin Tsohon Shugaban kasa, Muhammadu Buhari ne ta dauki nauyin Fulanin da suka takura ma yankinmu a Mulkinsa>>Inji Kungiyar Kare muradun Inyamurai ta Ohanaeze Indigbo

Ta bayyana a fili cewa, Gwamnatin Tsohon Shugaban kasa, Muhammadu Buhari ne ta dauki nauyin Fulanin da suka takura ma yankinmu a Mulkinsa>>Inji Kungiyar Kare muradun Inyamurai ta Ohanaeze Indigbo

Duk Labarai
Kungiyar kare muradun Inyamurai ta Ohanaeze Indigbo ta bayyana cewa Gwamnatin tsohon shugaba kasa, Muhammadu Buhari ce ta dauki nauyin fulanin da suka rika damun yankinsu da hare-haren. Kungiyar tace tun bayan da shugaba Buhari ya sauka a mulki sannan ya bar Duniya Fulani suka daina kai musu hare-haren da suke kai musu. Mataimakin shugaban kungiyar, Mazi Okechukwu Isiguzoro da me magana da yawun kungiyar, Chief Thompson Ohia ne suka bayyana hakan. Sun bayyana cewa, Rikicin ya lakume rayukan mutane 2,960 a yankin nasu.
Da Duminsa: Kwankwaso ya zabi wanda yake son yayi takarar gwamnan Kano a ADC, kuma jam’iyyar ta amince masa

Da Duminsa: Kwankwaso ya zabi wanda yake son yayi takarar gwamnan Kano a ADC, kuma jam’iyyar ta amince masa

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, kamin komawarsa ADC, Kwankwaso ya bukaci a bashi damar kawo wanda zai yi takarar Gwamnan jihar Kano. Saidai jam'iyyar ADC tace ya kamata a bari a yi zabe dan baiwa duka masu ra'ayin tsayawa takara bayyana aniyarsu. Saidai Rahoton yace Kwankwaso ya dage cewa shi dai a bashi damar ya kawo wanda zai tsaya takara. ADC din dai a karshe ta amince masa. Rahoton wanda ya fito daga kafar the Whistler yace Kwankwaso Nasiru Yusuf Gawuna yake son tsayarwa a ADC ya fuskanci Abba a 2027.
Kalli Bidiyon yanda ‘Yan Kwankwasiyya suna ta ihun Peter Obi yayin da ya halarci wajan taron komawar Kwankwaso ADC

Kalli Bidiyon yanda ‘Yan Kwankwasiyya suna ta ihun Peter Obi yayin da ya halarci wajan taron komawar Kwankwaso ADC

Duk Labarai
An ga 'yan Kwankwasiyya na ta ihun Peter Obi a yayin da Peter Obin ya halarci wajan taron komawar Kwankwaso Kwankwaso jam'iyyar ADC. Kwankwaso dai ya yanki katin komawa ADC inda aka ga ya dagashi sama yana nunawa mabiyansa. Atiku tuni yace yana maraba da kokawar Kwankwaso ADC. https://twitter.com/i/status/2038606520649199731