Thursday, April 16
Shadow
Kalli Bidiyon yanda mutanen gari suka daka wawa a wajan taron yakin neman zaben shugaba Tinubu a jihar Bayelsa

Kalli Bidiyon yanda mutanen gari suka daka wawa a wajan taron yakin neman zaben shugaba Tinubu a jihar Bayelsa

Duk Labarai
Bidiyon ya bayyana kan yanda mutane suka daka wawar fastoci da katakan da aka yi amfani dasu a wajan taron yakin neman zaben shugaba Tinubu a jihar Bayelsa. Bidiyon da ya watsu sosai a kafafen sada zumunta inda aka ga mata da maza na wawar fastocin da katakan kowa yana daukar nasa. Lamarin ya jawo zazzafar muhawara. https://twitter.com/i/status/2044737240698351839
Kotu ta bukaci a nemo mata Tsohuwar ministar Jinkai, Sadiya Umar Farouk Ruwa a jallo, saboda ta ki zuwa kotu wajan da ake Shari’ar ta ta zarginta da satar dala Miliyan $1.3 da Naira Miliyan 746.6

Kotu ta bukaci a nemo mata Tsohuwar ministar Jinkai, Sadiya Umar Farouk Ruwa a jallo, saboda ta ki zuwa kotu wajan da ake Shari’ar ta ta zarginta da satar dala Miliyan $1.3 da Naira Miliyan 746.6

Duk Labarai
A zaman kotun dake Abuja da aka yi a yau, Alhamis 16 ga watan Afrilu na ci gaba da shari'ar tsohuwar ministar Jinkai, Sadiya Umat Frouk. Sadiya da dayan wanda ake zargin me suna Bashir Nura Alkali wanda shine babban sakatare a ma'aikatar basu samu halarta ba. Na ukunsu, Sani Nafiu Mohammed ne kadai ya samu halartar zaman kotun. Dan hakane kotun tace a kamosu duk inda suke. Ana dai zarginsu ne da sama da fadi da wasu rarar kudade na dala Miliyan $1.3 wanda ya kamata a ce an mayar da kudaden asusun gwamnati amma sai suka saka a aljihunsu. Sannan akwai wasu kudaden suma da suka kai Naira N746,574,303 da ake zarginsu da sacewa. Jimulla ana musu zarge-zarge guda 21. Ita dai Sadiya ta bayyana cewa ta je neman lafiya ne kasar Saudiyya shiyasa aka jita shiru.
‘Yan Arewa bayin Allah ruwa Kwata suke sha, sai da Peter Obi ya tausaya ya je ya gina musu fanfon burtsatse sannan suke samun ruwan sha me kyau>>Inji Wannan masoyiyar Peter Obin

‘Yan Arewa bayin Allah ruwa Kwata suke sha, sai da Peter Obi ya tausaya ya je ya gina musu fanfon burtsatse sannan suke samun ruwan sha me kyau>>Inji Wannan masoyiyar Peter Obin

Duk Labarai
Wata masoyiyar Peter Obi ta dauki hankula bayan data bayyana cewa kamin shigar Peter Obi Arewa, Mutanen Arewa, Ruwan Kwata suke sha. Tace zuwan Peter Obi ne har ya ginawa 'yan Arewa fanfon Burtsatse. Tace abin ban tausai, bata taba tunanin akwai mutane irinta masu shan ruwan kwata ba. https://twitter.com/i/status/2044554314715111524
Nafiu Bala ya fara bin dattawan Arewa dan su sulhuntashi dasu Atiku

Nafiu Bala ya fara bin dattawan Arewa dan su sulhuntashi dasu Atiku

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Nafiu Bala Gombe ya fara bin dattawan Arewa akan su sulhuntashi dasu Atiku. Hakannna zuwane bayan da Su Atikun suka ce sun koreshi daga jam'iyyar ADC sannan rahotanni suka bayyana cewa, masu daukar nauyinsa sun yi watsi dashi. Rahoton yace saidai su Atikun sun ce ai shi yanzu ba dan ADC bane kuma basu tare da makaryaci wanda baya cika Alkawari. https://twitter.com/i/status/2044662504195014749
Da Duminsa:Ranar Zabe ko sakamakon zabe ba zan batawa kaina Lokaci in dubaba saboda nasan nine zan yi nasara, A lokacin kana da wasu tsirarin Gwamnoni tare da kai na yi nasara akanka ballantana yanzu da baka da Gwamna ko daya tare dakai>>Tinubu ya gayawa Atiku

Da Duminsa:Ranar Zabe ko sakamakon zabe ba zan batawa kaina Lokaci in dubaba saboda nasan nine zan yi nasara, A lokacin kana da wasu tsirarin Gwamnoni tare da kai na yi nasara akanka ballantana yanzu da baka da Gwamna ko daya tare dakai>>Tinubu ya gayawa Atiku

Duk Labarai
Fadar shugaban kasa tawa Tsohon Ministan shugaban kasa, Atiku Abubakar zazzafan martani game da kalamansa na cewa shine zai yi nasara a zaben 2027. A martanin da me baiwa shugaban kasa shawara kan harkar sadarwa, Daniel Bwala ya baiwa Tinubu, Yace a zaben 2023 ma lokacin Atiku nada wasu tsirarin Gwamnoni a bayansa an yi nasara akansa. Ballantana yanzu da bashi da gwamna ko guda daya. Yace dan haka yasan Shugaba Tinubu ba zai ma bata lokacinsa ya duba sakamakon zabe ba ranar zabe dan yasan shine zai yi nasara. https://twitter.com/i/status/2044540151842415010
Allah me Iko:Kalli Bidiyon yanda dandazon kudan zuma ya mamaye wasu sassa na kasar Israyla

Allah me Iko:Kalli Bidiyon yanda dandazon kudan zuma ya mamaye wasu sassa na kasar Israyla

Duk Labarai
Rahotanni daga kasar Yahudawan Israyla na cewa wasu dandazon kudan zuma sun bayyana inda aka ga sun mamaye wasu sassa na kasar. Bidiyon faruwar lamarin ya mamayr kafafen sadarwa inda mutane ke ta muhawara akai. Wasu dai sun rika danganta abin da cewa, kamun Allah ne, wasu kuma suka ce sakayya ce. https://twitter.com/i/status/2044431481162875143