Tuesday, April 21
Shadow
Kalli Bidiyon: Ashe Ministan Kudi, Wale Edun, Karyata shugaba Tinubu yayi shiyasa aka saukeshi

Kalli Bidiyon: Ashe Ministan Kudi, Wale Edun, Karyata shugaba Tinubu yayi shiyasa aka saukeshi

Duk Labarai
A dazune dai hutudole ya kawo muku rahoton cewa, Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya sauke ministan kudi, Wale Edun daga mukaminsa. Gwamnati dai bata bayyana dalilin sauke shi daga mukamin nasa ba a hukumance. Lamarin ya zowa mutane da mamaki duk da yake cewa a kwanakin baya an yi ta rade-radin cewa, Ministan yayi fama da rashin lafiya. Saidai a yanzu a kafafen sada zumunta, ana ta yada wani Bidiyo daya nuna shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu yana cewa sun cimma yawan kudin shiga da suke nema a shekarar 2025. Saidai a wani Bidiyo daban kuma, an ga Ministan kudin, Wale Edun na cewa Tiriliyan 40 suke nema a shekarar 2025 amma kudin shiga Tiriliyan 10 kacal suke tsammani. Wannan magana ta ci karo data shugaban kasa, wadda wannan yasa wasu ke ta hasashen cewa, dalili kenan da yasa...
Da Duminsa: Shugaba Tinubu ya sauke Ministan Kudi da Ministan gidaje

Da Duminsa: Shugaba Tinubu ya sauke Ministan Kudi da Ministan gidaje

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya sauke Ministan Kudi, Wale Edun da Ministan Gidaje Da ci gaban birane Umar Dangiwa. Sakataren Gwamnati, Sanata George Akume ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar. An baiwa Wale Edun umarnin ya mikawa karamin Ministan kudi, Mr. Taiwo Oyedele ragamar ma'aikatar. Hakanan shugaba Tinubu ya nada Mr. Muttaqha Rabe Darma (PhD) a matsayin Ministan Gidaje da ci gaban birane.
Kalli Bidiyon: A yaune Nafiu Bala Gombe ke gudanar da baban taron Jam’iyyar ADC tsagin da yake shugabanta amma babu kowa a wajan

Kalli Bidiyon: A yaune Nafiu Bala Gombe ke gudanar da baban taron Jam’iyyar ADC tsagin da yake shugabanta amma babu kowa a wajan

Duk Labarai
Rahotanni sun ce a yaune Nafiu Bala Gombe yake gudanar da babban taron jam'iyyar ADC tsaginsa inda zasu zabi shuwagabannin jam'iyyar. Saidai Bidiyon dake ta yawo a kafafen sada zumunta aun nuna cewa babu kowa a wajan taron Wasu rahotanni sun ce har Naira Dubu hamsin ake baiwa duk wanda ya yadda zai je wajan taron amma duk da haka babkowa. https://twitter.com/i/status/2046526118052651202
Babbar Kotun jihar Kaduna ta sake daga sauraron bayar da belin Malam Nasiru Ahmad El-Rufai sai zuwa watan June

Babbar Kotun jihar Kaduna ta sake daga sauraron bayar da belin Malam Nasiru Ahmad El-Rufai sai zuwa watan June

Duk Labarai
Da alama dai Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ba zai samu damar halartar zaben fidda gwani na jam'iyyar ADC ba. Saboda Mai shari'a Darius Khobo na babbar kotun jihar Kaduna ya sake daga sauraron belinsa sai satin farko na wajan Yuni. ICPC na ci gaba da tsare malam Nasiru Ahmad El-Rufai inda ake zarginsa da almundahanar kudade da aikata ba daidai ba da mukamin da ya samu na Gwamna da sauransu. Jam'iyyar ADC dai ta tsayar da karshen watan Afrilu zuwa Mayu dan gudanar da zaben fidda gwani.
Wallahi Wannan karon Kanawa ba zasu yi Kwankwaso ba>>Inji Asari Dokubo

Wallahi Wannan karon Kanawa ba zasu yi Kwankwaso ba>>Inji Asari Dokubo

Duk Labarai
Tsohon dan tsageran Naija Delta daya tuba ya ce zai shiga gaba wajan yin yakin neman zaben kada a zabi Kwankwaso a Kano. Yace wallahi wannan karon Kanawa zasu baiwa Kwankwaso mamaki dan ba zasu yi shi ba. Yace Kwankwaso yana tunanin zai sayar da Kanawa ne a farashin kwabo kwabo? Ya bayyana hakane a wani Bidiyonsa da ya watsu a kafafen sada zumunta. https://twitter.com/i/status/2046484892951687502
Farashin Dala a Kasuwar Chanji ta yau, Talata

Farashin Dala a Kasuwar Chanji ta yau, Talata

Duk Labarai
Farashin dala a kasuwar Chanji ta Gwamnati a yau, Talata, 21 ga watan Afrilu ta kamane akan Naira 1345.47 kan kowace dala. Farashin ya dan tashi zuwa Naira 1,345.87 akan kowace dala inda daga baya ya koma farashin sama. A kasuwar bayan fage kuwa ta garuruwan Abuja, Legas da Kano farashin dala ya farane akan Naira 1390 zuwa Naira 1,405.