Thursday, February 6
Shadow
YANZU YANZU: An Binciko yadda Nuhu Ribaɗu yayi Awun gaba da wasu Biliyoyin kuɗaɗe a lokacin da yake shugaban Hukumar EFCC, inji Fitaccen mai Binciken nan Dr. Idris

YANZU YANZU: An Binciko yadda Nuhu Ribaɗu yayi Awun gaba da wasu Biliyoyin kuɗaɗe a lokacin da yake shugaban Hukumar EFCC, inji Fitaccen mai Binciken nan Dr. Idris

Duk Labarai
Nasan wanda yake Sauyawa Nuhu Ribaɗu Dalar Amurka na cin hanci da rashawa. Fitaccen mai bincike kuma mai fafutukar kare haƙƙin bil'adama a ɗan asalin Najeriya, mazaunin kasar Ingila, Dr. Idris Ahmed ya bayyana wasu muhimman zarge-zarge da ya sani akan Malam Nuhu Ribadu mai taimakawa Shugaban kasa kan sha'anin tsaron Najeriya. Dr. Idris ya bayyana cewa, “A lokacin da yake shugaban hukumar EFCC, ya karbi makudan kudaden cin hanci. Musammab dalar Amurka, akwai wani wanda Shi ne me yiwa Nuhu Ribadu canjin dalar Amurka, wanda tsohon dan sanda, ne ACP mai ritaya ne ana kiransa da suna (retired) Rabiu Abubakar Shariff. Rabiu Abubakar Shariff shi clasmate dina ne lokacin muna karatun sakandare. Shine wadda Lieutenant General Tukur Buratai ya turo shi zuwa kasar Burtaniya, domin ya saci sa...
YANZU YANZU: Sabida tsohon Allah da nake dashi a lokacin Mulkina Ko Fentin Gidana Ban Canja Ba A Tsawon Shekaru Takwas Da Na Yi Akan Mulki, Cewar Buhari

YANZU YANZU: Sabida tsohon Allah da nake dashi a lokacin Mulkina Ko Fentin Gidana Ban Canja Ba A Tsawon Shekaru Takwas Da Na Yi Akan Mulki, Cewar Buhari

Duk Labarai
Tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari ya bayyana cewa a tsawon mulkin da ya yi shekara takwas, ko sake fentin gida bai yi ba . Buhari ya faɗi haka ne a lokacin da ƙungiyar ƴan jarida reshen kafofin yaɗa labarai a Katsina suka kai masa ziyara a gidansa dake garin Daura. Ya ce yana cikin ƙoshin lafiya idan aka kwatanta shi da abokansa da suka taso tun suna yara, inda wasu daga cikinsu da sanda suke dogarawa su yi tafiya. Ya kuma ce Mataimakin Shugaban ƙasa, kashin Shattima ne ya fidda kuɗi daga aljihunsa ya ke gyara masa gidansa na Kaduna. “Da zarar an kammala gyaran gidan zan koma kaduna”, inji Buhari. Tunda da farko, shugaban tawagar ƴan jaridun, Yusuf Ibrahim Jargaba ya faɗa wa tsohon shugaban ƙasar cewa sun kawo masa ziyarar ban girma ne da kuma yi masa ban gajiya. Jar...
DA DUMI DUMINSA; Za’a ƙirƙiri Sabbin Jahohi guda 31, Mun samu bukatar ƙirƙiro sabbin Jihohi 31 a Najeriya – Kalu

DA DUMI DUMINSA; Za’a ƙirƙiri Sabbin Jahohi guda 31, Mun samu bukatar ƙirƙiro sabbin Jihohi 31 a Najeriya – Kalu

Duk Labarai
Kwamitin gyaran kundin tsarin mulki na Majalisar wakilan Najeriya, ya ce ya karbi buƙatar ƙirƙiro jihohi 31 daga sasan kasar, domin ƙara yawan jihohin da ake da su akan 36 dake wanzuwa yanzu haka. Shugaban kwamitin Benjamin Kalu, wanda shi ne mataimakin shugaban Majalisar wakilai, ya bayyana haka a zaman majalisar.Kalu ya ce bukatun sun hada da 6 daga Arewa ta Tsakiya, 4 daga Arewa ta Gabas, 5 daga Arewa ta Yamma, sai kuma 5 daga Kudu maso Gabas da 4 daga Yankin Kudu maso Kudu da 7 daga Kudu maso Yamma.Ga jerin bukatun kamar yadda Kalu ya bayyana. Jihar Okun daga Kogi Jihar Okura daga Kogi Jihar Confluence daga Kogi Jihar Benue Ala daga Benue Jihar Apa daga Benue Jihar FCT daga FCT Jihar Amana daga Adamawa Jihar Katagum daga Bauchi Jihar Savannah daga Borno J...
Shiekh Professor Isa Ali Pantami ya biyawa ‘yar marigayi Sheikh Albani bashin da ake binta bayan ya jagoranci yin sulhu

Shiekh Professor Isa Ali Pantami ya biyawa ‘yar marigayi Sheikh Albani bashin da ake binta bayan ya jagoranci yin sulhu

Duk Labarai
Malam Isa Ali Pantami ya jaddada wa jagorancin Darul Hadith cewa, dole su zauna da dukkan daliban Malam Albaniy da suka kora daga Darul Jadith ayi sulhu a samu mafita, idan ba haka ba Malam yace da kansa zai jagoranci gurfanar dasu a Kotu har zuwa Supreme Court zai dauki nauyin shari'ah. Sannan Malam Isa Ali Pantami ya tabbatar da case din Aisha 'yar Malam Albaniy wacce aka damfareta kudi Kimanin Naira Miliyan 10, ta biya Miliyan 5 ya rage saura Miliyan 5, mun nema mata taimako ta account dinta na Stanbic IBTC, kuma jama'a kun hada mata kudi kimanin Naira Miliyan 2 da dubu dari uku da wani abu kamar yadda zaku gani a hoto. To nan take Malam Isa Ali Pantami a gurin da ya jagoranci zama dasu ya sa PA dinsa ya tura wa Aisha sauran kudi Naira Miliyan 3 da dubu dari uku ta account dinta n...
YANZU-YANZU: Shugaban Ƙasa Bola Tinubu Ya Amince Da Naɗin Dakta Asiya Balaraba Ganduje A Matsayin Darakta A Hukumar Raya Arewa Maso Yamma

YANZU-YANZU: Shugaban Ƙasa Bola Tinubu Ya Amince Da Naɗin Dakta Asiya Balaraba Ganduje A Matsayin Darakta A Hukumar Raya Arewa Maso Yamma

Duk Labarai
DAGA Bashir Abdullahi El-bash A wani mataki na duba cancanta da ƙwazon aiki, shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya amince da naɗin Dakta Asiya Abdullahi Umar Ganduje a matsayin daraktar sashen kula da al’umma da raya yankunan karkara a sabuwar hukumar raya yankin Arewa maso Yamma. Naɗin Dakta Asiya Ganduje a wannan matsayi ajiye ƙwarya ne a gurbinta duba da cewa mace ce jaruma mai juriya da himmar aiki. Ta daɗe tana ɗawainiya da hidimtawa al’umma ta fannoni daban-daban na rayuwa daga aljihunta. Ta ba da gagrumar gudunmawa wajen raya ilimi na addini da na zamani a birane da karkara. Ta taimaki ɗumbin jama’a da tallafin karatu, aikin yi, sana’o’in dogaro da kai da harkokin kula da kiwon lafiya da ayyukan jinƙai. Dakta Asiya Ganduje ba a iya nan ta tsaya ba, mace ce mai kaifin ƙwaƙwalwa...
Dansandan Najeriya ya Kkashe kansa

Dansandan Najeriya ya Kkashe kansa

Duk Labarai
Dansandan Najeriya a Ofishin 'yansandan dake Mada jihar Nasarawa ya harbi kanshi ya kashe kansa. Rahotanni sunce a ranar da ya kashe kansa, anga dansandan me suna Dogara Akolo-Moses yana yawo abinsa. Shaidu sun ce ya shiga wani daki ne ya kulle ya harbi kansa a cikin ofishinsu, kuma karar harbin da abokan aikinsa suka ji ne yasa suka ruga da gudu zuwa cikin dakin da yake. Nan take suka iskeshi kwance a cikin jini. Zuwa yanzu dai ba'a san dalilin da yasa ya kashe kansa ba. Kakakin 'yansandan jihar, Ramhan Nansel ya tabbatar da faruwar lamarin inda yace ana kan bincike.
Idan kuka sake kuka kkasheni zaku dandana kudarku>>Trum ya gayawa Iran

Idan kuka sake kuka kkasheni zaku dandana kudarku>>Trum ya gayawa Iran

Duk Labarai
Shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya gargadi kasar Iran da cewa idan suka sake suka kasheshi zasu dandana kudarsu. A baya dai lokacin Trump yana yakin neman zabe an kaiwa Trump hari inda aka so kasheshi saidai ya tsallake rijiya da baya inda kuma aka zargi cewa kasar Iran ce ta kai masa harin. Saidai tuni kasar Iran ta fito ta karyata wannan zargin da ake mata inda tace ba itace ta kaiwa Trump hari ba. Wasu masu sharhi kan al'amuran yau da kullun sun bayyana cewa, watakila kasar ta Amurka na wannan maganane saboda kawai tana son fara yakin kai tsaye da kasar Iran.
Innalil-Lahi wa’inna iLaihi rajiun: Allah ya yiwa dalibai almajirai (17) Rasuwa Agarin Kauran-Namoda sanadiyyar Gobara wadda ta shafe awa uku tana ci

Innalil-Lahi wa’inna iLaihi rajiun: Allah ya yiwa dalibai almajirai (17) Rasuwa Agarin Kauran-Namoda sanadiyyar Gobara wadda ta shafe awa uku tana ci

Duk Labarai
Innalillahi wa Inna Ilaihi rajiun ibtila'in gobarar wuta yayi sanadiyyar mutuwar almajirai fiyeda 15 tareda jikkata wasu a daren jiya makantar malan ghali bakin kasuwa dake Kauran Namoda Jihar Zamfara. Rahotanni da muke samu shine wutar ta auku ne a daren ranar Talata kuma Almajirai da yawa sun jikkata. Hasbunallahu wa ni'imatil wakell.Ubangiji Allah shi gafarmasu ya bamu iKon cinye Wannan jarabawa.
Trump yace Fàlàsdìnàwà su fice daga Gaza saboda America nason kwace Gazar da sake yi mata ginin zamani

Trump yace Fàlàsdìnàwà su fice daga Gaza saboda America nason kwace Gazar da sake yi mata ginin zamani

Duk Labarai
Donald Trump ya firgita Falasɗinawa kan shawarwarinsa game da makomar zirin Gaza, saboda ya ce Amurka za ta ƙwace iko da zirin tare sauya fasalinsa. Wannan ne sauyi mafi girma game da manufofin Amurka kan yankin gabas ta tsakiya cikin gomman shekaru. Trump ya bayyana hakan ne a taron manema labarai a fadar White House tare da firaiministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu. "Amurka za ta ƙarbi ikon zirin Gaza kuma za mu mallake zirin kuma mu dauki alhalin kwance nakiyoyin da aka dąsa sannan kuma gyara wuraren da aka lalata," in ji Trump. Nan da nan firaiministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu ya nuna jin dadinsa ga kalaman na Mr Trump, inda ya ce hakan zai canza tarihi. Netanyahu ya ce "ina kara maimaitawa, muradinmu uku ne kuma na uku shi ne tabbatar da cewa zirin Gaza bai kara za...
Karya kika min, ban taba cewa, Tinubu Barawo ba>>Nuhu Rubadu ya gayawa Naja’atu Muhammad inda yace ta tabbatar ta fito ta bashi Hakuri nan da kwanaki 7

Karya kika min, ban taba cewa, Tinubu Barawo ba>>Nuhu Rubadu ya gayawa Naja’atu Muhammad inda yace ta tabbatar ta fito ta bashi Hakuri nan da kwanaki 7

Duk Labarai
Me baiwa shugaban kasa shawara akan harkar Tsaro, Malam Nuhu Ribadu ya bayyana cewa, Maganar da Naja'atu Muhammad ta yi akan cewa ya taba cewa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu barawo ba gaskiya bane. Bidiyon da ya watsu a Tiktok ya dauki hankula sosai inda akai ta martani kala-kala. Naja'atu Muhammad ta bayyana cewa, Nuhu Ribadu ya yi wannan magana ne a lokacin yana shugaban hukumar EFCC. Saidai lauyan Nuhu Ribadu, Dr Ahmed Raji, SAN ya bayyana cewa maganar Naja'atu ba gaskiya bane kuma suna neman nan da kwana 7 ta fito ta bayar da hakuri. Sun ce idan bata yi hakan ba, basu da zabi da ya wuce su kaita kotu.