Wednesday, March 25
Shadow
Da Duminsa:Ana yada rade-radin cewa, Sheikh Khalifa Sani Zaria ya rigamu gidan gaskiya a hannun jami’an tsaron dake tsare dashi

Da Duminsa:Ana yada rade-radin cewa, Sheikh Khalifa Sani Zaria ya rigamu gidan gaskiya a hannun jami’an tsaron dake tsare dashi

Duk Labarai
Tauraron Tiktok kuma dan siyasa, Warkal ya bayyana cewa, suna samun rahotanni wanda basu tabbata ba cewa, Sheikh Khalifa Sani Zaria ya rigamu gidan gaskiya a hannun jami'an tsaron dake tsare dashi. Ya bayyana cewa, idan har hakan ta tabbata, to lallai ba zasu sake zaben shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ba. https://www.tiktok.com/@ameenwarkal/video/7621190147920399623?_r=1&_t=ZS-94zDN7p0QjZ&sp_source=7537614245375297080
Gwamnatin Najeriya tamin alkawarin bani jirgin ruwan danyen man fetur 15 a wata amma guda 5 kawai suke bani>>Inji Dangote

Gwamnatin Najeriya tamin alkawarin bani jirgin ruwan danyen man fetur 15 a wata amma guda 5 kawai suke bani>>Inji Dangote

Duk Labarai
Attajirin Najeriya, Aliko Dangote ya bayyana cewa, Gwamnatin Tarayya ta masa alkawarin bashi jirgin ruwan danyen mai guda 15 a wata. Yace amma bata cika wannan alkawari ba, Jirage 5 kawai take bashi a wata. Dangote ya nemi Gwamnatin data cika Alkawarin data daukar masa. Yace matatarsa na fitar da gangar tataccen man fetur 650,000 a kullun kuma yana biyawa Najeriya dama Afrika bukatar man fetur dinsu
Maganar komawar Gawuna Kwankwasiyya na shirin tabbata, ji kalman Yabo sa Kwankwaso ke gaya ma gawunan

Maganar komawar Gawuna Kwankwasiyya na shirin tabbata, ji kalman Yabo sa Kwankwaso ke gaya ma gawunan

Duk Labarai
Tsohon Gwamnan Kano, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso ya jinjinawa Gawuna sosai a yayin da tawagar gawunan suka je masa gaisuwar Sallah. An ji Kwankwaso na fadar cewa Gawuna kwamishinansa ne me daraja kuma yanda yake girmamashi tun yana gwamna har yau bai canja ba. Sannan yace Gawuna bai taba fadar wata magana mara dadi akansa ba. https://twitter.com/i/status/2036720937874108685 Rade-radi dai sun yi yawa akan cewa, Gawuna na shirin komawa Kwankwasiyya inda Ake tsammanin Kwankwason zai tsayar dashi takarar gwamna.
Duk da saukar farashin mai a kasuwannin Duniya, ‘Yan kasuwar man fetur na Najeriya sun ki rage farashi

Duk da saukar farashin mai a kasuwannin Duniya, ‘Yan kasuwar man fetur na Najeriya sun ki rage farashi

Duk Labarai
Rahotanni na cewa a kasuwar Duniya, Farashin danyen man fetur ya fadi zuwa dala $100 daga dala $130. Saidai duk da hakan, 'yan kasuwar man fetur din na Najeriya suna ci gaba da sayar da man da tsada a farashin Naira 1,300 akan kowace lita. Saukar farashin a kasuwar Duniya ya farune a yayin da ake tsammanin tattaunawar sulhu tsakanin Amurka da Iran zata haifar da da me ido. Saidai duk da wannan, gidajen man fetur a Najeriya ciki hadda na gwamnati, NNPCL suna sayar da man akan farashi sama da Naira 1,300 a wasu gidajen man ma har sama da hakan. Hauhawar farashin man fetur din a Najeriya yasa an samu hauhawar wasu kayan masarufi dama ababen hawa.
Farashin dala a kasuwar Chanji a yau, Laraba

Farashin dala a kasuwar Chanji a yau, Laraba

Duk Labarai
Farashin dala a kasuwar Chanji a yau Laraba, 25 ga watan Maris ya fara ne da 1,375.26. Saidai da gari ya kara wayewa ya dan tashi zuwa Naira ₦1,375.61 akan kowace dala. Wannan a kasuwar Gwamnati kenan kuma yana kasa da farashin ₦1,390 da aka sayar da dalar jiya Talata. Farashin Dalar a kasuwar bayan fage a Legas da Abuja kuwa yana tsakanin Naira ₦1,420 zuwa ₦1,435 ne.
Kalli Bidiyon: Bature ya zargi shugaba Tinubu da daukar hayar mutane a kasar Ingila aka basu Fan £500 dan su fito titi su tarbi shugaban kasar

Kalli Bidiyon: Bature ya zargi shugaba Tinubu da daukar hayar mutane a kasar Ingila aka basu Fan £500 dan su fito titi su tarbi shugaban kasar

Duk Labarai
Wannan baturen ya zargi Gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da cewa, ta biya mutane a kasar fan £500 dan su fito kan titi su yabawa Gwamnatin Tinubu. A kwanakin da ya gabata ne dai shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya je kasar Ingila inda ya gana da Gwamnatin kasar akan alakar Najeriya ta kasuwanci da kasar. https://twitter.com/i/status/2036344540169118035
Allah Sarki Kalli Bidiyon: Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana abinda zai fara yi idan ICPC suka sakeshi

Allah Sarki Kalli Bidiyon: Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana abinda zai fara yi idan ICPC suka sakeshi

Duk Labarai
Bayan zaman kotun da aka yi dashi a Jihar Kaduna jiya, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya zanta da 'yan Jarida. Inda ya gayawa jaridar Daily Trust cewa, idan ya fito, sune na farko da zai yi hira dasu. https://www.tiktok.com/@luperasom/video/7620960315328564487?_r=1&_t=ZS-94yZA08QohV&sp_source=7537614245375297080 A jiya ne dai ICPC ta gurfanar da malam Nasiru Ahmad El-Rufai a kotu inda aka zargeshi da almundahanar kudade wanda ya karyata.
Kalli Bidiyon: Wannan wulakancin da ake mana, wataran ba za’a yi ba>>inji Matar ElRufai, Asia yayin da aa hanata shiga cikin kotun da ake masa shari’a

Kalli Bidiyon: Wannan wulakancin da ake mana, wataran ba za’a yi ba>>inji Matar ElRufai, Asia yayin da aa hanata shiga cikin kotun da ake masa shari’a

Duk Labarai
An ga matar tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai, Hajiya Asia a kofar kotun da ake masa shari'a inda aka hanata shiga. An ji tana fadar cewa, Rayuwace, wannan ma wataran zai wuce. Daga baya dai an shigar da ita cikin kotun ta hanyar baya. https://www.tiktok.com/@luperasom/video/7620898661421026578?_r=1&_t=ZS-94yYA7QAZyD&sp_source=7537614245375297080 A jiya ne dai ICPC suka gurfanar da tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai a kotu inda ake tuhumarsa kan zarge-zargen almundahanar kudade.
Allah Sarki, Kalli Bidiyon Tauraruwar fina-finan Hausa na neman Taimakon Ali Nuhu a mata aiki saboda rashin Lafiyar dake damunta

Allah Sarki, Kalli Bidiyon Tauraruwar fina-finan Hausa na neman Taimakon Ali Nuhu a mata aiki saboda rashin Lafiyar dake damunta

Duk Labarai
Wannan wata Tauraruwar fina-finan Hausa ce da ta fito ta bayyana cewa, Qari ya fito mata a hannu sannan take neman taimakon Ali Nuhu, Abba El-Mustapha da sauransu su taimaka mata a mata aiki. An ga Bidiyon nata a kafafen sada zumunta inda ya dauki hankula da yawa sun tausaya mata. https://www.tiktok.com/@i_a_sarari/video/7620898247309102356?_r=1&_t=ZS-94yWZthM0wa&sp_source=7537614245375297080
Kalli Bidiyon: Kada mu sake zabar Wannan Azzalumar Gwamnatin ta Tinubu saboda basu son Arewa kuma ga Haraji>>Inji Tauraron  fina-finan Hausa, Sadik Sani Sadik

Kalli Bidiyon: Kada mu sake zabar Wannan Azzalumar Gwamnatin ta Tinubu saboda basu son Arewa kuma ga Haraji>>Inji Tauraron fina-finan Hausa, Sadik Sani Sadik

Duk Labarai
Tauraron fina-finan Hausa, Sadiq Sani Sadiq yayi kira ga 'yan Arewa kada su sake zaben gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu saboda azzaluma ce. Sadiq ya bayyana hakane a wani Bidiyonsa daya dauka a wata kasuwa inda aka ga yana magana cikin fushu. Ya zargi gwamnatin Tinubu cewa bata son Arewa, inda yace sun kawo haraji da Rashin Tsaro. Ya karkare maganarsa da cewa kada a sake zaben Tinubu a matsayin shugaban kasa inda yace idan kunne yaji.... https://www.tiktok.com/@kamalkmann/video/7620830467448720660?_r=1&_t=ZS-94y3ShKLgNF&sp_source=7537614245375297080