Wannan wani malamin Kirista ne da ya karbi kalmar Shahada inda yace sunansa Evangelist Peter.
Amma yace yanzu ya canja suna zuwa Malam Anas.
https://www.tiktok.com/@umsamultimediatv/video/7603310895640530184?_r=1&_t=ZS-93g676Oda0v
Wani mutum me suna Okon Micheal da matarsa tace ya saketa bayan da suka yi shekaru 2 da aure ya huce haushinsa akan mahaifiyar matarsa
Dama dai ya ginawa surukar tasa gida.
Ai kuwa matar tasa na cewa ta samu wanda take so ya saketa .
Sai ya je gidan da ya ginawa surukar tasa ya rusheshi.
Shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya jinjinawa matar shugaban kasa, Remi Tinubu inda ya bayyanata a matsayin wadda ake girmamawa sosai.
Ya bayyana hakane a addu'a ta musamman da aka shirya yiwa kasa a Amurka.
https://twitter.com/i/status/2019472178551370215
Gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde ya kunyata matarsa a yayin da ta yi yunkurin sumbatarsa a bainar jama'a.
An ga matar ta duka zata sumbaceshi amma ya kawar da kansa.
Hakan ya faru har sau biyu.
Lamarin ya farune a wajan bikin cikar jihar Oyo shekaru 50 da kafuwa.
https://twitter.com/i/status/2019423145242059002
An ga dan gidan tsohon shugaban jam'iyyar APC kuma tsohon gwamnan Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje me suna Abdulaziz ya kaiwa Kwankwaso ziyara.
Wani karin abin daukar hankali shine an ganshi da jar hula.
An dai ta yin sharhi akan lamarin.
https://twitter.com/i/status/2019369705354719525
Tsohon Gwamnan Kano, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso ya je yiwa 'yan kasuwar Sinja jajen Ibtila'in da ya fada musu.
An ga yanda jama'a da yawa suka taru inda suke nuna soyayya da goyon baya a gareshi.
https://twitter.com/i/status/2019390309113950298
Rahotanni sun bayyana cewa kungiyar lauyoyin Najeriya, NBA sun ce zasu aikawa da hukumar 'yansandan Najeriya da sauran jami'an tsaro korafi dan a biciki tsohon gwamnan Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso kan wani ikirari da yayi.
Kungiyar ta bayyana hakane bayan zaman kwamitin zartarwasta, watau NEC
Sakataren kungiyar ta NBA, Etaba Agbor ne ya bayyana hakan a shafinsa na X.
Maganar da ake zargin Kwankwaso da yi shine, yace a shakerar 2019 ya dauki Abba Kabir Yusuf zuwa ganin alkalan kotun koli ta Najeriya bayan da hukumar zabe me zaman kanta, INEC ta bayyana zaben Kano a matsayin Inconclusive, watau wanda bai kammalu ba.
A karshe dai kotun kolin ta tabbatarwa da Gwanduje a wancan lokacin cewa shine yaci zaben.
Wannan magana ta tayar da hankuka musamman tsakanin Lauyoyin Najeri...
Rahotanni sun bayyana cewa, hukumar zabe me zaman kanta, INEC tawa jam'iyyun siyasa biyu Rijista.
Shugaban INEC din, Joash Amupitan ne ya bayyana haka a wajan wani taro na musamman a Abuja.
Yace jam'iyyun da akawa Rijistar sune, Democratic Leadership Alliance (DLA) da the Nigeria Democratic Congress (NDC).
Yace wasiku 171 ne aka gabatar na neman yiwa sabbin jam'iyyu rijista amma guda 2 ne kadai daga cimi suka tsallake.
An hangi wasu sojojin Najeriya tare da sojojin kasar Amurka da suka zo tayasu aiki suna daukar hotunan Selfie.
Hotunan sun dauki hankula a kafafen sada zumunta.
https://twitter.com/i/status/2019339118749397106
Bayan da tsohon Ministan Sadarwa, Farfesa Isa Ali Pantami ya je ofishin jam'iyyar APC na jihar Gombe ya sabunta rijistarsa a matsayin dan jam'iyyar APC.
A wajan ya bayyana cewa tun shekarar 2001 yake a siyasa amma ba da rigar siyasa ba.
Saidai wani tsohon Bidiyon sa da yake wa'azi akan Munbari wanda rahotanni suka ce an daukeshi ne a shekarar 2008, Pantami yace shi ba dan siyasa bane.
Wannan tsohon Bidiyon da aka zakulo ya kawo muhawara da cece-kuce sosai a kafafen sada zumunta.
https://twitter.com/i/status/2019190444131750239
https://www.tiktok.com/@mohammed_isa_hassan/video/7603075407704755476?_r=1&_t=ZS-93fbWQqLyYD
https://www.tiktok.com/@mohammed_isa_hassan/video/7603075407704755476?_r=1&_t=ZS-93fbWQqLyYD