Saturday, April 11
Shadow
Bayan da aka shafe kwana da kwanaki ana neman matar auren nan, a karshe dai an iske ta a dakin Otal ita da Qartonta suna shakatawa

Bayan da aka shafe kwana da kwanaki ana neman matar auren nan, a karshe dai an iske ta a dakin Otal ita da Qartonta suna shakatawa

Duk Labarai
Wata matar aure me suna Mrs Tilewa Olatunde Funke 'yar kimanin shekaru 42 ta bace ana ta nemanta. Lamarin ya farune a garin Ilara-Mokin na jihar Ondo. Saidai da bincike ya tsananta, 'yan sanda sun ganota a dakin otal da wani me suna Isa Alaba dan kimanin shekaru 55 a dakin otal suna shakatawa. Hukumar 'Yansandan ta bayyana cewa matar da kanta ta kai kanta wajan mutumin ba garkuwa yayi da ita ba kuma an warware matsalar cikin ruwan sanyi. Hukumar 'Yansandan ta yi kira ga mutane dasu daina yada labaran da basu inganta ba kan lamarin.
Da Duminsa: Sabon rikici ya kunno kai a jam’iyyar ADC inda wani babban mutum shima ya maka su David Mark da Aregbesola a kotu yace ba halastattun shugabannin jam’iyyar bane

Da Duminsa: Sabon rikici ya kunno kai a jam’iyyar ADC inda wani babban mutum shima ya maka su David Mark da Aregbesola a kotu yace ba halastattun shugabannin jam’iyyar bane

Duk Labarai
Dan majalisar wakilai, Leke Abejide wanda dan jam'iyyar ADC ne ya maka shuwagabannin jam'iyyar na riko David Mark, da Rauf Aregbesola a kotu inda yace kotu ta saukesu. Hakan na zuwane a yayin da ake tsaka da fama da rikicin Nafiu Bala. Ya shigar da karar ne a gaban babbar kotun tarayya dake Abuja inda kotun ta tsayar da ranar 13 ga watan Afrilu dan yanke hukunci. Jam'iyyar ADC na fuskantar kalubale kala-kala inda take zargin hannun APC a lamarin.
Haduwata ta farko da Atiku ya bani kyautar Naira Miliyan 20>>Inji Fati Muhammad

Haduwata ta farko da Atiku ya bani kyautar Naira Miliyan 20>>Inji Fati Muhammad

Duk Labarai
Tsohuwar Tauraruwar fina-finan Hausa, Fati Muhammad ta bayyana cewa, ta hadu da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar kuma ya bata kyautar Naira Miliyan 20. Ta bayyana hakane a wata hira da aka yi da ita, wadda Ali Jita ya jagoranta. Saidai tace kudin bata yi wani abun azo a gani dasu ba yawanci mutane ta rika saiwa kyautuka. https://www.tiktok.com/@amanardondaalbishir/video/7626912177827400981?_r=1&_t=ZS-95RhhfRixJB
Ji Sautin Murya: Tinubu ba kudi ya bani na masa yakin neman zabe ba, tunda na sanshi ba ko ruwan Fiya wata bai taba bani kudi na siya ba>>Inji Malam Nasiru Ahmad El-Rufai

Ji Sautin Murya: Tinubu ba kudi ya bani na masa yakin neman zabe ba, tunda na sanshi ba ko ruwan Fiya wata bai taba bani kudi na siya ba>>Inji Malam Nasiru Ahmad El-Rufai

Duk Labarai
Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana cewa, ba kudi Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bashi ya masa yakin neman zabe ba. Yace shi tunda yasan Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu bai taba bashi ko sisi ba ko da kudin siyen Pure Water. Yace amma ba zai iya rantsuwa akan sauran wadanda sukawa Tinubu yakin neman zabe ba amma shi dai ba'a bashi ko sisi ba. https://twitter.com/i/status/2042551635289739358
INEC ta tabbatar da David Mark a matsayin shugaban jam’iyyar ADC

INEC ta tabbatar da David Mark a matsayin shugaban jam’iyyar ADC

Duk Labarai
Lauyan David Mark, Realwan Okpanachi ya tabbatar da cewa a takardar rantsuwa da hukumar zabe me zaman kanta, INEC ta gabatarwa da kotu. Ta tabbatar da cewa, David Mark ne halastaccen shugaban jam'iyyar ADC hakanan Rauf Aregbesola shine halastaccen sakataren jam'iyyar. Ya bayyana hakane ga manema labarai bayan zaman kotun. A yanzu dai kotu ce za'a jira ta yanke hukunci kan karar. https://twitter.com/i/status/2042698761843912756
Ikon Allah: Kalli Bidiyon yanda Sojojin dake cikin tawagar yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu suka kaure da fada suna dukan Juna

Ikon Allah: Kalli Bidiyon yanda Sojojin dake cikin tawagar yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu suka kaure da fada suna dukan Juna

Duk Labarai
A yau ne shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya kai ziyara jihar Bayelsa. A cikin tawagar motocin dake masa rakiya, an ga wasu sojoji sun tsaya a hanya suna dambe. Bidiyon lamarin ya dauki hankula sosai a kafafen sada zumunta inda da yawa ke cewa hakan bai dace ba. https://twitter.com/i/status/2042690556531257589
Yanda aka shirya munafurcin Tsigeni a matsayin Gwamna da hadin Bakin Mataimakina, Gwarzo, dan ya gajeni>>Inji Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf

Yanda aka shirya munafurcin Tsigeni a matsayin Gwamna da hadin Bakin Mataimakina, Gwarzo, dan ya gajeni>>Inji Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf

Duk Labarai
Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya bayar da labarin yanda aka shirya munafurcin tsigeshi a matsayin Gwamna tare da hadin gwiwar mataimakinsa da ya sauka, Gwarzo. Gwamnan yace an shirya tsigeshi ne sai kuma Gwarzo ya maye gurbinsa. Yace amma sai Allah bai basu nasara ba. Gwamnan ya bayyana hakane a yayin ganawa da wasu magoya bayansa. Yace yaji ance mataimakin nasa ya sauka daga mukaminsa amma har yanzu shi bai ga takardar ajiye aikin nasa ba.