Tuesday, April 21
Shadow
Wallahi Wannan karon Kanawa ba zasu yi Kwankwaso ba>>Inji Asari Dokubo

Wallahi Wannan karon Kanawa ba zasu yi Kwankwaso ba>>Inji Asari Dokubo

Duk Labarai
Tsohon dan tsageran Naija Delta daya tuba ya ce zai shiga gaba wajan yin yakin neman zaben kada a zabi Kwankwaso a Kano. Yace wallahi wannan karon Kanawa zasu baiwa Kwankwaso mamaki dan ba zasu yi shi ba. Yace Kwankwaso yana tunanin zai sayar da Kanawa ne a farashin kwabo kwabo? Ya bayyana hakane a wani Bidiyonsa da ya watsu a kafafen sada zumunta. https://twitter.com/i/status/2046484892951687502
Farashin Dala a Kasuwar Chanji ta yau, Talata

Farashin Dala a Kasuwar Chanji ta yau, Talata

Duk Labarai
Farashin dala a kasuwar Chanji ta Gwamnati a yau, Talata, 21 ga watan Afrilu ta kamane akan Naira 1345.47 kan kowace dala. Farashin ya dan tashi zuwa Naira 1,345.87 akan kowace dala inda daga baya ya koma farashin sama. A kasuwar bayan fage kuwa ta garuruwan Abuja, Legas da Kano farashin dala ya farane akan Naira 1390 zuwa Naira 1,405.
Kalli Bidiyon: A samu wani ya taimakamin da kudin mota, Saurayi ne ya kirani naje Lagos, da naje sai yace ban masa ba in koma garin mu, gashi banda ko sisi>>Inji Wannan matar

Kalli Bidiyon: A samu wani ya taimakamin da kudin mota, Saurayi ne ya kirani naje Lagos, da naje sai yace ban masa ba in koma garin mu, gashi banda ko sisi>>Inji Wannan matar

Duk Labarai
Wannan matar ta dauki hankula a kafafen sada zumunta inda tace Saurayi ya kirata, ta tashi daga Ibadan taje Lagos wajansa. Tace amma da taje wajansa sai yace bata masa, ta mai tsufa. Tace ya koreta yace ta koma garinsu, inda tace gashi a yanzu bata da kudin mota. https://twitter.com/i/status/2046121249798062177
Kalli Bidiyon: Mijina yace zai kara aure nace ya sakeni, ba wai dan kishi ba saidai dan baya iya gamsar dani, a sati sau daya muke yi>>Inji Umm Faizan

Kalli Bidiyon: Mijina yace zai kara aure nace ya sakeni, ba wai dan kishi ba saidai dan baya iya gamsar dani, a sati sau daya muke yi>>Inji Umm Faizan

Duk Labarai
Ummu faizan ta bayar da labarin cewa, tsohon mijinta yace zai kara aure inda ita kuma ta nemi ya saketa. Tace ba wai dan kishi ba, sai dan baya iya gamsar da ita rayuwar aure. Tace wani lokacin a sati sau daya kawai suke yi. Tace duk da haka ta hakura ta dauka kaddararta kenan, kuma lura da cewa, sun haihu. Tace kwatsam sai yace zai kara aure, tace sai take ganin itama ya kasa gamsar da ita, ya zai iya gamsar da mata 2. Tace dalili kenan yasa ta nemi ya saketa, tace da ya kaita kara gurin iyayenta da abokai, amma da mahaifinta ya ji dalili sai ya goyi bayanta. Tace ta samu ta sake aure kuma sabon mijin data aura yana gamsar da ita gashi har ta dauki ciki. Tace matar da tsohon Mijinta ya aura itama ta rabu dashi. Tace sai gashi yana kiranta wai ta kashe auren da ta y...