Thursday, April 30
Shadow
Kalli Bidiyon: Tauraruwar kudancin Najeriya data kawowa mijinta kawarta ya biya bukatarsa dasu a daki daya kuma suka dauki Bidiyon ta sake sakin wani sabon Bidiyon

Kalli Bidiyon: Tauraruwar kudancin Najeriya data kawowa mijinta kawarta ya biya bukatarsa dasu a daki daya kuma suka dauki Bidiyon ta sake sakin wani sabon Bidiyon

Duk Labarai
A jiya ne dai muka samu Labarin cewa, Sisi Alagbo wadda ta kaiwa mijinta kawarta ya biya bukata dasu a daki daya kuma suka dauki Bidiyon, Bidiyon ya watsu a kafafen sada zumunta. Sisi dai ta fito ta bayar da hakuri inda tac abinda suka yi ita da mijin nata kuskurene da ba zai sake faruwa ba. Saidai wani abin mamaki shine, Sisi ta sake sakin wani Sabon Bidiyon. A Bidiyon data saki an ganta tana tallar wani maganin karfin maza wanda take cewa wai ko namiji zai biya bukatarsa da mata biyu ne a tare wannan magani zai masa aiki. Wannan yasa da yawa suka rika zargin cewa, Bidiyon farko ma itace ta sakeshi kuma da gangan dan ta samu daukaka ta ci gaba da sayar da maganinta https://twitter.com/i/status/2049509952180322751
Kalli Bidiyon: Dalilin da yasa bamu baiwa Unguwannin Talakawa isashshiyar wuta shine Almubazzaranci suke da wutar>>Inji Wani jami’in NEPA

Kalli Bidiyon: Dalilin da yasa bamu baiwa Unguwannin Talakawa isashshiyar wuta shine Almubazzaranci suke da wutar>>Inji Wani jami’in NEPA

Duk Labarai
Wani jami'in hukumar wutar lantarki ya bayyana cewa dalilin da yasa basu baiwa Unguwannin talakawa isashshiyar wuta shine Almubazzaranci suke da wutar. Yace a unguwannin talakawa ne da zarar an kawo wuta sai kaga sun kumma Borehole, sun yi guga, an kunna Freezer an kumma electric cooker, wutar da ya kamata a sha a sati daya sai su shanyeta a kwana daya. https://twitter.com/i/status/2049554848517890253
Da Duminsa: Matarnan data jagoranci daga jan dan kamfai a Kano wanda suka sakawa sunan dan kamfan tsula ta samu mukamin siyasa a jihar Kano

Da Duminsa: Matarnan data jagoranci daga jan dan kamfai a Kano wanda suka sakawa sunan dan kamfan tsula ta samu mukamin siyasa a jihar Kano

Duk Labarai
Fatima Naseer Teemahcool wadda itace shugaban Gida-Gida na Tiktok wadda kuma itace ta jagoranci daga jan dan kamfai a Kano wanda suka sakawa sunan dan kamfan tsula ta samu mukamin siyasa. Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa, shugaban karamar hukumar Nasarawa, Yusuf Imam Ogan Boye ne ya bata shugabar harkokin mata na karamar Hukumar. Rahoton yace a yau, Alhamis ne takardar bata mukamin ta fito. Ta dai fito ta bayar da hakuri kan daga dan kamfai din data yi inda tace ba zata sake aikatawa ba
Kalli Bidiyon: Mun yaba da mulkin Tinubu da tausayin talakawa da yake yi, mu musulmai da Kiristocin Jihar Filato zamu sake zabensa>>Inji Sheikh Sani Yahya Jingir

Kalli Bidiyon: Mun yaba da mulkin Tinubu da tausayin talakawa da yake yi, mu musulmai da Kiristocin Jihar Filato zamu sake zabensa>>Inji Sheikh Sani Yahya Jingir

Duk Labarai
Babban malamin Addinin Islama a Jihar Filato, Sheikh Sani Yahya Jingir ya bayyana cewa sun yaba da mulki irin na shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu. Musamman ma wajan tausayin talakawa. Yace dan haka yace Musulmai da Kiristoci na jihar ta Filato zasu sake zabensa. https://twitter.com/i/status/2049758928846630971
Anata Rade-radin cewa APC ta hana Pantami Tikitin takarar Gwamna a jihar Gombe

Anata Rade-radin cewa APC ta hana Pantami Tikitin takarar Gwamna a jihar Gombe

Duk Labarai
Rade-radi na ta yawo a kafafen sada zumunta cewa jam'iyyar APC ta hana farfesa Isa Ali Pantami tikitin takarar Gwamna a jihar Gombe. Wasu sun bayyana mamakin hakan inda wasu kuma suka ce hakan bai basu mamaki ba sun san dama ba zai samu ba. https://twitter.com/i/status/2049750766173217208 https://twitter.com/i/status/2049552036182598135 https://twitter.com/i/status/2049579383258591559
Kalli Bidiyon: Musa Mai Sana’a ya yiwa Ali Jita zazzafan martani bayan da Ali Jita yayi magana akan tallata gwamnatin APC da yake yi

Kalli Bidiyon: Musa Mai Sana’a ya yiwa Ali Jita zazzafan martani bayan da Ali Jita yayi magana akan tallata gwamnatin APC da yake yi

Duk Labarai
Tauraron fina-finan Hausa, Musa Mai Sana'a yawa Ali Jita Zazzafan Martani kan maganar da yayi game da tallata Gwamnatin APC da yake yi. Ali Jita yace ya gayyaci Musa Mai Sana'a ya zo zauren tattaunawarsa dan ya amsa wasu tambayoyi game da tallata APC da yake yi amma bai je ba. Saidai a nasa maganar, Musa Mai Sana'a yace Ali Jita ya fita daga harkar rayuwarsa dan bai san yanda yake ciyar da iyalansa ba. Musa yace bai taba tambayar Ali Jita ba ya taimakeshi kuma shima da yace wasu 'yan siyasa suka bashi tallafi wa ya dameshi? https://www.tiktok.com/@maisanaakanotv/video/7634237707656498453?_r=1&_t=ZS-95xjDhJA6Rl
Kalli Bidiyon: Matashi ya tafi Abuja daga Kaduna a kasa dan zuwa jinjinawa shugaba Tinubu cewa aikinsa na kyau ba yunwa ba matsalar tsaro musamman a Arewa

Kalli Bidiyon: Matashi ya tafi Abuja daga Kaduna a kasa dan zuwa jinjinawa shugaba Tinubu cewa aikinsa na kyau ba yunwa ba matsalar tsaro musamman a Arewa

Duk Labarai
Wani matashi daga Kaduna, ya fara tattaki zuwa Abuja a kasa dan zuwa ya jinjinawa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu kan kokarin da yake. Matashin yace babu yunwa babu matsalar tsaro a Arewa. Hakan na zuwane yayin da al'umma da yawa ke kukan cewa matsalar tsaro ta yi kamari musamman a yankin Arewa sannan kuma ga matsin rayuwa. https://www.tiktok.com/@agg_multimedia_services/video/7633896950009580818?_r=1&_t=ZS-95xiR4EWQIT
Jam’iyyar ADC ta bayyana matakin da zata dauka bayan da Kotu tace kada INEC ta yadda da sabbin shuwagabannin ta

Jam’iyyar ADC ta bayyana matakin da zata dauka bayan da Kotu tace kada INEC ta yadda da sabbin shuwagabannin ta

Duk Labarai
Jam'iyyar ADC reshen su David Mark, Atiku, Kwankwaso da sauransu, sun bayyana matakin da zasu dauka bayan da kotu tace kada INEC ta yadda da zaben da suka gudanar na zabar shuwagabannin su. A sanarwar daya fitar me magana da yawun jam'iyyar ADC, Bolaji Abdullahi ya bayyana cewa, zaben shuwagabannin da suka yi be soke shuwagabancin jam'iyyar a matakin jihohi ba. Inda suka ce shuwagabannin jihohi na jam'iyyar zasu ci gaba da shugaban cinsu har su kammala. Saidai Bolaji Abdullahi yace sun samu hukuncin kotun kuma zasu nemi lauyoyinsu su basu shawara kan abinda ya dace su yi.