Tuesday, March 17
Shadow
Kalli Bidiyon: Me bakin Kiys da danta da ya dauki hankula sosai inda suke tallar kayan gyaran jikin mata tare

Kalli Bidiyon: Me bakin Kiys da danta da ya dauki hankula sosai inda suke tallar kayan gyaran jikin mata tare

Duk Labarai
Wannan Bidiyon Tauraruwar, Me bakin Kiyss ce tare da danta inda aka ga suna tallar kayan gyaran Jikin mata tare. An ganta tana juya Qirji da Mazaunanta a gaban dan nata wanda hakan ya matukar dauki hankula. Shima dan an ji yana tallar kayan gyaran jikin matan wanda sai an hada da batsq a gaban mahaifiyar tasa. Da yawa dai sun yi Allah wadai inda wasu ke cewa Allah ya rabamu da Bariki. https://www.tiktok.com/@mebakinkiss18/video/7618135572552469778?_r=1&_t=ZS-94lmZmwgO6j&sp_source=7537614245375297080
Da Duminsa: Gwamnatin tarayya ta kawo tsarin hawa jirgin sama bashi, daga baya mutum ya rika biya a hankali

Da Duminsa: Gwamnatin tarayya ta kawo tsarin hawa jirgin sama bashi, daga baya mutum ya rika biya a hankali

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya ta hanyar (CREDICORP) ta kawo tsarin hawa jirgin sama bashi yanda mutum zai rika biya a hankali. (CREDICORP) ce ta sanar da hakan a shafinta na X inda kuma tace ta yi wannan shiri ne da hadin gwiwar manhajar MyVisaro, idan mutum na bukatar hawa jirgin da gaggawa bashi da kudi, kawai zai shiga manhajar MyVisaro ne ya bayyana aniyarsa. Saidai akwai tantancewa, dan tabbatar da mutum ya cika wasu sharuda kamin bashi damar hawa jirgin kyauta. Gwamnatin tace ta kawo wannan tsari ne dan saukakawa 'yan Najeriya musamman ma a yayin da wata tafiya ta gaggawa ta samesu.
Da Duminsa: Za’a mayar da Malam Nasiru Ahmad El-Rufai gidan gyara hali na Kaduna bisa sabbin zarge-zargen da ake masa

Da Duminsa: Za’a mayar da Malam Nasiru Ahmad El-Rufai gidan gyara hali na Kaduna bisa sabbin zarge-zargen da ake masa

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa hukumomi na shirin mayar da malam Nasiru Ahmad El-Rufai jihar Kaduna dan ci gaba da tsareshi a can. Hakan na zuwane yayin da ake shirin fara shari'ar sa akan wasu sabbin zarge-zargen da ake masa. Hakan ya fito ne daga Sahara Reporters inda tace ta samu rahoton daga majiya me karfi. Saidai bata bayyana sabbin zarge-zargen da akewa El-Rufai ba. Majalisar jihar ta Kaduna dai ta bayyana yin bincike da gano aikata ba daidai ba a zamanin Malam Nasiru Ahmad El-Rufai na Gwamnan Kaduna. A yanzu dai malam Nasiru Ahmad El-Rufai na tsarene a hannun Hukumar ICPC.
Da Duminsa:Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya aikawa kotu da korafi kan wata Mugunta da take hakkinsa da ake masa a ofishin ICPC

Da Duminsa:Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya aikawa kotu da korafi kan wata Mugunta da take hakkinsa da ake masa a ofishin ICPC

Duk Labarai
Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya aikewa da kotun Magistrate dake Abuja da korafin cewa, ana kokarin take masa hakkinsa a matsayinsa na dan kasa. ElRufai yayi zargin cewa, shugaban Hukumar ICPC din Musa Adamu Aliyu ta hannun wasu yaransa ya bayyana masa cewa sharadin sakinsa shine sai idan ya amince zai daina shiga harkar siyasa. El-Rufai ta hannun Lauyansa yace wannan kokarine na take masa hakkinsa a matsayinsa na dan kasa wanda ba zai lamunta ba. Zuwa yanzu dai Hukumar ta ICPC bata ce uffan ba kan zargin da malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya mata.