Tuesday, January 21
Shadow
Za’a samu saukin rayuwa, kayan masarufi zasu sauka kasa>>Inji Gwamnatim tarayya

Za’a samu saukin rayuwa, kayan masarufi zasu sauka kasa>>Inji Gwamnatim tarayya

Duk Labarai
Ministan kudi da tattalin arziki, Wale Edun ya bayyana cewa a shekarar 2025 za'a samu saukin hauhawar farashin kayan masarufi. Yace alkaluman hauhawar farashin kayan masarufi zasu yi kasa zuwa kaso akalla 15 cikin 100 inda a yanzu suke a maki 34.8 kamar yanda hukumar kididdiga ta kasa, NBS ta bayyana. Ya bayyana hakane a Abuja ranar Litinin yayin kaddamar da kwamitin kula da kudi inda yace zasu cimma burin samun kudin shiga na Naira Tiriliyan 47.9 da suka saka a gaba a shekarar 2025. Yace babban bankin Najeriya, CBN ya saka burin rage hauhawar farashin kayan abinci zuwa kaso 15 cikin 100 a cikin shekarar nan kuma zasu dage dan cimma wannan buri.
Kalli Bidiyo: An hango me kamfanin Facebook, Mark Zuckerberg na kallon Nonuwan matar me kamfanin Amazon a wajan taron rantsar da Donald Trump a matsayin shugaban kasa

Kalli Bidiyo: An hango me kamfanin Facebook, Mark Zuckerberg na kallon Nonuwan matar me kamfanin Amazon a wajan taron rantsar da Donald Trump a matsayin shugaban kasa

Duk Labarai
Abinda me kamfanin Facebook, Mark Zuckerberg yayi a wajan rantsar da shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya dauki hankula. Bidiyo ya nuna Mark Zuckerberg yana kallon nonuwan matar me kamfanin Amazon, watau Jeff Bezos. Lamarin ya jawo cece-kuce sosai inda wasu ke ganin itama bai kamata ta yi irin wannan shigar ta nuna kirji ba a wajan taro me muhimmanci irin wannan ba. https://www.tiktok.com/@musicedits304/video/7462128836424092946?_t=ZM-8tFH4LH9YBh&_r=1 Kalli Bidiyin anan Manyan masu kudin Duniya da suka mallaki kamfanonin sadarwa dana kasuwanci irin su Facebook, Amazon, Tiktok, Apple da saransu duk sun halarci wajan taron rantsar da Donald Trump.
Donald Trump ya sha rantsuwa a matsayin shugaban Amurka na 47

Donald Trump ya sha rantsuwa a matsayin shugaban Amurka na 47

Duk Labarai
Donald Trump ya sha rantsuwa a matsayin shugaban Amurka na 47, bayan nasarar da ya yi a zaɓen shugaban ƙasar na 2024. An rantsar da Donald Trump ne a cikin ginin Majalisar Dokokin ƙasar na Capitol, karon farko a cikin shekaru. Gabanin Trump, an rantsar da mataimakinsa, kuma tsohon mai sukarsa, JD Vance. Jim kaɗan bayan shan ranstuwa, Trump ya sanar da wasu tsauraran matakai da zai ɗauka, musamman a ɓangaren tsaron iyaka da kuma rage kwararar baƙi zuwa ƙasar. Wani abin kuma shi ne yadda Trump ya riƙa sukar magabacinsa, Joe Biden, a gabansa, jim kaɗan bayan shan rantsuwa. Donald Trump ya dawo kan mulki ne bisa alƙawarin kawo tsauraran sauye-sauye waɗanda suka sha bamban da na Biden. A jawabinsa na farko, Trump ya ce ''Sabon babin ci gaban Amurka zai fara ne daga yau''. '...

Maganin warin baki

Magunguna
Idan ana son yin maganin warin baki ga hanyoyin da masana kiwon lafiyar baki suka bayar da shawarar ya kamata a bi dan samun nasara. A rika wanke baki da goge harshe duk bayan an kammala cin abinci, akwai abin goge harshe na musamman da ake sayarwa, kuma da yawa burushin goge baki ana yinsa ta yanda mutum zai iya amfani dashi wajan goge harshe amma mutane da yawa basu sani ba. Ka duba bayan burushin goge bakinka, idan kaga yana da kurzuni-kurzuni ko kaushi to alamace zaka iya juya bayan ka goge harshenka dashi duk bayan kammala cin abinci. Hakanan masana kiwon lafiyar baki da hakora sun bada shawarar rika yin sakace ana cire abinci da ya makale a tsakanin hakora duk bayan kammala cin abinci dan kawar da warin baki. Hakanan ana son mutum ya rika canja burushin wanke baki akai-ak...
Coci a jihar Delta ta kori Reverend Fr. Daniel Okanatotor saboda ya je kasar Amurka yayi aure a boye wanda a dokar kiristanci bashi ba aure tunda ya kai mukamin Priest

Coci a jihar Delta ta kori Reverend Fr. Daniel Okanatotor saboda ya je kasar Amurka yayi aure a boye wanda a dokar kiristanci bashi ba aure tunda ya kai mukamin Priest

Duk Labarai
Coci a jihar Delta ta dakatar da Fr. Daniel Okanatotor saboda zuwa kasar Amurka yayi aure a boye wanda a dokar kiristanci tunda ya kai matsayin Priest, to bashi ba aure har ya mutu. Cocin me suna The Catholic Diocese of Warri ta sanar da cewa ta dakatar da Fr. Daniel daga mukamin Priest a wata sanarwa data fitar ranar 16 ga watan Janairu Tace Fr. Daniel ya sanar da ita cewa zai ajiye mukamin na Priest, saidai tace kamin ta kammala sauke masa mukamin, sai kawai ta ji labarin yayi aure. Dan haka ne ta sanar da dakatar dashi.
Kwata-Kwata gwamnatin ka bata da tausayin talaka>>Kungiyar Kwadago ta Soki Tinubu kan kara farashin man fetur

Kwata-Kwata gwamnatin ka bata da tausayin talaka>>Kungiyar Kwadago ta Soki Tinubu kan kara farashin man fetur

Duk Labarai
Kungiyar kwadago ta NLC ta soki Gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu saboda abinda ta kira rashin tausai bayan kara farashin man fetur. Wani jigo a NLC ne ya bayyanawa jaridar Punchng haka a yayin da kungiyar 'yan kasuwar man fetur din ke cewa ba laifinsu bane maganar karin kudin man fetur din. Hakanan kuma matatar man fetur ta Dangote ta bayyana cewa, karin farashin man fetur din ya samo asaline daga hauhawar farashin danyen man fetur wanda dashine ake yin man fetur din. A ranar Juma'a data wuce, an sayar da man fetur din akan farashin Naira 1050 zuwa Naira 1150 akan kowace lita. Mataimakin shugaba kungiyar kwadago ta NLC, Prof Theophilus Ndubuaku ya bayyana cewa, ya kamata shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a duk sanda irin bukatar abu haka ta taso ya rika saka masu ruwa ...
Wata sabuwar Kungiya me cike da hadari da bata yadda da kowane irin addini ba ta bayyana a Kaduna

Wata sabuwar Kungiya me cike da hadari da bata yadda da kowane irin addini ba ta bayyana a Kaduna

Duk Labarai
Hukumar kula da shige da fici a Najeriya, NIS ta bayyana samuwar wata kungiya me suna ACHAD a jihar Kaduna. Rahotanni sun bayyana cewa Kungiyar na neman mabiya kuma bata yadda da wani addinin Musulunci ko na Kiristanci ba. Hakanan an bayyana cewa kungiyar na safarar mutane musamman kananan yara. An jawo hankalin mutane da su gaggauta sanar da hukumomi da zarar sun ga abinda basu ganemawa ba.
Matashi ya sha duka, yana fuskantar barazanar kkisa saboda yana yawan kunna wakokin Rarara

Matashi ya sha duka, yana fuskantar barazanar kkisa saboda yana yawan kunna wakokin Rarara

Duk Labarai
Bayan Ya Šha Dukan Tsiya Akan Yawan Kunna Wakokin Rarara, Yanzu Kuma An Soma Ýi Màsa Baŕazanaŕ Ķìšà Matashi Atiku dan jihar Kano na fuskantar barazana sakamakon kwashe tsawon lokaci da ya yi yana nuna soyayya tare da kunna wakokin Mawaki Rarara a shagonsa, lamarin da ya jawo masa dukan tsiya daga wasu matasan Unguwa. Rahotanni na cewa yanzu haka wannan matashin ya gagara zuwa shagon sa inda gudanar da kasuwancin sa sakamakon barazanar da ýake fuskantar daga wasu matasa. Yanzu haka dai matashin na shan magunguna tun bayan lokacin da aka lakada masa duka domin ya samu rauni da dama a jikinsa.
Umma Shehu tasa an kama shehun Tiktok saboda kazafın zina

Umma Shehu tasa an kama shehun Tiktok saboda kazafın zina

Duk Labarai
Umma shehu tasa an kama shehun tiktok saboda kazafın zina {"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} A kwanakin baya ne Shehun Tiktok yai wani Video inda ya ambaci sunan Umma Shehu tare da kafe hoton ta yace itace take daurewa zina gindi ake yinsa ko yaushe. Kalaman nasa sunyi tsauri wanda yasa ta ɗauki matakin gaggawa kuma ta bayyana cewa ba zata yafe masa ba har sai an ƙwata mata hakkin ta. Ga bidiyon nasa: Dannanan da Kallo https://www.tiktok.com/@suba_neh/video/7457878476910087430?_t=ZM-8tBvk6AoQ5O&_r=1 ...
Wata Sabuwa: Ana Rade-Radin Gwamnatin Tinubu ta tursasa tsohon shugaban kasa, Muhammad Buhari zuwa kotu, saidai gwamnatin tace maganar sirri ce

Wata Sabuwa: Ana Rade-Radin Gwamnatin Tinubu ta tursasa tsohon shugaban kasa, Muhammad Buhari zuwa kotu, saidai gwamnatin tace maganar sirri ce

Duk Labarai
Wasu rade-radi sun bayyana a kafafen sada zumunta cewa gwamnatin tarayya ta bukaci tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya je wata kotu a kasar Faransa yayi bayani. An shigar da wata karane kan aikin tashar wutar lantarki ta Mambila inda ake neman Dala Biliyan $6. Saidai a martanin da me magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuna ya fitar yace wannan magana ba haka take ba. Ya tabbatar da cewa, an shigar da kara wanda ake yinsa a sirri kuma duka manyan mutanen da suka je suka yi bayani a wajan kotun, sun yi hakanne bisa radin kansu da kuma nuna kishin kasa amma ba gwamnatin tarayya ce ta tursasasu ba. Ya kara da cewa, ko kadan bai kamata ace an wallafa labarin shari'ar ba saboda ta sirri ce har sai kotu ta kammala bincikenta. Saidai yace gwamnatin na godiya ga duka wadand...