Wednesday, February 4
Shadow
Kalli Bidiyon:Yanda Sakataren jam’iyyar APC na jihar Gombe ya tashi a gaban Farfesa Isa Ali Pantami yace duk ‘yan jam’iyyar APC na jihar haushin Pantami suke ji

Kalli Bidiyon:Yanda Sakataren jam’iyyar APC na jihar Gombe ya tashi a gaban Farfesa Isa Ali Pantami yace duk ‘yan jam’iyyar APC na jihar haushin Pantami suke ji

Duk Labarai
A yau ne aka tashi da rahoton cewa, farfesa Isa Ali Pantami ya je jihar Gombe dan ya sabunta rijistarsa ta zama dan jam'iyyar APC. Ya samu tarba me kyau tun daga filin jirgi, saidai kuma a ofishin jam'iyyar APC inda ya je yin rijistar an samu tangarda inda wasu suka yabeshi. Amma Sakataren jam'iyyar, Ibrahim Musa ya bayyana cewa, duk haushinsa suke ji dalili shine a baya bai taba zuwa ofishin jam'iyyar ba inda wasu ma cewa suka rika yi shi ba dan jam'iyyar bane. https://twitter.com/i/status/2019078323930824786
Kalli Bidiyon:Ganin Sanata Adams Oshiomhole tare da wata mata me yin irin fina-finan nan na Alfasha ya jawo cece-kuce sosai

Kalli Bidiyon:Ganin Sanata Adams Oshiomhole tare da wata mata me yin irin fina-finan nan na Alfasha ya jawo cece-kuce sosai

Duk Labarai
A jiya ne dai wani Bidiyon sanata Adams Oshiomhole tare da wata mata ya bayyana, inda aka ganshi yana mata tausa a kafarta. Da yawa abin ya daure musu kai dan dai an ga ba matarsa bace. Da bincike yayi tsanani, an gano matar tana fina-finan Bhqtsq Rahotanni sun ce matar daga kasar Afrika ta kudu take. Lamarin dai ya bayar da mamaki sosai. https://twitter.com/i/status/2018618286947352741
Kalli Bidiyon: Wata Kirista ta musulunta dalilin soyayyar da takewa Oga Abba

Kalli Bidiyon: Wata Kirista ta musulunta dalilin soyayyar da takewa Oga Abba

Duk Labarai
Wata Kirista ta bayyana cewa tana son mawaki OGAbbah wanda dalilin haka ya sanya ta musulunta. Ta bayyana masa hakane a comment bayan da ya wallafa Bidiyon wannan wakar a shafinsa na Tiktok. OgAbbah dai shine yayi wakar samu kudinka kawai ka kashe wadda ta watsu sosai a ciki da wajen Najeriya. Ya tambayeta cewa da gaske take abinda ta fada? Inda tace masa Eh da gaske take. yace to ta aika masa da DM https://www.tiktok.com/@ogabbah/video/7600814482528423186?_r=1&_t=ZS-93dZwrc6liT
Kalli Bidiyon: Kudin dana mallaka sun fi karfin Naira Biliyan 2>>Inji Soja Boy

Kalli Bidiyon: Kudin dana mallaka sun fi karfin Naira Biliyan 2>>Inji Soja Boy

Duk Labarai
Tauraron Mawakin Hausa, Soja Boy ya bayyana cewa, kudin da ya mallaka sun fi karfin Naira Biliyan 2. Ya bayyana hakane a hirar da Ali Jita yayi dashi inda yace dan haka dole yayi abinda yake so. https://www.tiktok.com/@arewa_realistic/video/7602534368900369682?_r=1&_t=ZS-93dXULQenhY Hakanan ya kara da cewa, Mawaki, Wizkid yafi Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa. Yace yanzu da Wizkid zai ce yana son ganawa da sarkin Saudiyya wani Malami yace yana son ganawa da sarkin, sai Wizkid ya riga malamin ganawa da sarkin. https://www.tiktok.com/@mr_ceedking/video/7602463541144177940?_r=1&_t=ZS-93dZ8iLRUH3
Da Duminsa: Kasar Amurka ta aiko da sojoji Najeriya

Da Duminsa: Kasar Amurka ta aiko da sojoji Najeriya

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, kasar Amurka ta aiko da sojoji zuwa Najeriya. Kafar Reuters ta bayyana cewa an aiko da sojojin na musamman zuwa Najeriya dan su taimaka wajan samar da tsaro. General Dagvin R.M. Anderson wanda shine shugaban rundunar sojojin Amurka a Afrika ya tabbatar da hakan. Ya bayyana cewa, sojojin ba masu yawa bane amma bai bayyana ko guda nawa bane. Sannan zuwa yanzu ba'a bayyana wace jihace aka tura sojojin.