Malam ya soki Farfesa Isa Ali Pantami da cewa, Duk Jami'ar data bashi mukamin Farfesa ta cuci kanta kuma yana bata mata suna.
https://www.tiktok.com/@prettyme_barrister/video/7610862067440012564?_r=1&_t=ZS-94FEjAojgi8
Tauraron Kannywood, Garzali Miko ya halarci gidan abokin aikinsa, Nuhu Abdullahi inda sua yi shan ruwa acan.
An ji yana jinjinawa Nuhu yana fadar cewa, gashi ga me kudi.
https://www.tiktok.com/@garzalimiko/video/7610895597519785237?_r=1&_t=ZS-94F5Em9fboO
https://www.tiktok.com/@kb_international/video/7610527513944591623?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7610527513944591623&source=h5_m×tamp=1772111994&user_id=7483197776647635989&sec_user_id=MS4wLjABAAAAN7fVbcc0mzRzgIxdVwTekj-Bzgfq381B8aILPWs15fqP6aFNZ5GwIpbLEwMTYvVW&item_author_type=2&social_share_type=0&utm_source=copy&utm_campaign=client_share&utm_medium=android&share_iid=7606977366144993025&share_...
Wannan yanda wutar Lantarki ta daukene yayin da sabon shugaban 'yansanda ke shirin fara jawabi.
Ana ta dau muhawa inda wasu ke cewa, wani ne ya kashe wutar ba tare da ya sani ba inda wasu kuma ke cewa wutace aka dauke.
https://twitter.com/i/status/2026892411457118480
Rahotanni sun bayyana cewa a ranar 24 ga watan Fabrairu, wasu mutane 2 wanda ba musulmai ba sun shiga babban masallacin Manchester dake kasar Ingila yayin da ake tsaka da sallar Tarawih.
Masallatan sun kama daya da wasu maqamay a hannunsa an bayyana mutumin a matsayin dan kimanin shekaru 40 inda kuma dayan ya tsere har yanzu ana nemansa.
Babu dai rahoton cewa, wani ya jikkata ko rasa rai.
Firaiministan Ingila, Keir Stermer yayi Allah wadai da lamarin inda ya jinjinawa wadanda suka kama daya daga cikin masu laifin.
Ya bayyana cewa sun ware kudi har fan Miliyan £40 dan samar da karin tsaro a masallatai da makarantun Islamiya, da kuma yankunan da musulmai suke.
Rahotanni sun ce masallacin ya dauki matakan tsaro dan kiyaye kara faruwar hakan
https://twitter.com/i/status/...
Wannan wani mahaifine da ke aiki a wajan hakan ma'adanai da ya tara kudi ya saiwa 'ya'yansa Talabijin(TV) da suka dade auna son ya sai musu.
A nan ya sai musu talabijin dinne, kuma yanda suka saki baki suna kallo shine ya dauki Bidiyonsu ya watsawa Duniya.
Da yawa sun jinjina masa.
https://twitter.com/i/status/2026424085127823521
Wannan dan majalisar wakilai daga jihar Kanone da aka raka da ihun bama yi da jifa a mazabarsa.
The Cable tace dan majalisa me wakiltar Dawakin Tofa/Tofa/Rimin Gado ne watau Tijjani Jobe akawa wannan abin.
An ga yanda matasa ke zaginsa suka jifarsa da duwatsu.
https://twitter.com/i/status/2026040436440097055
Rahotanni sun bayyana cewa, babbar kotun tarayya dake Abuja ta saurari karar da Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya shigar inda yake kalubalantar tsareshi da ake yi da kuma zarge-zargen da ake masa.
Me magana da yawun Malam Nasiru, Muyiwa Adekeye ne ya bayyana hakan inda yace a yau, Kotun na sauraren karar take hakkin malam da ya shigar.
Kotu taji duka bangarorin me kara da wanda ake kara inda ta daga karar zuwa ranar 27 ga watan February dan baiwa wanda ake karar damar tattara bayanai.
https://twitter.com/i/status/2026602579300360622
Sabon Shugaban 'yansandan Najeriya, Olatunji Disu kenan a wannan Bidiyon inda ya sarawa mahaifiyarsa bayan da aka bashi mukamin IGP.
An ga yanda suka rungumi juna bayan da ya sarawa mahaifiyar tasa.
https://twitter.com/i/status/2026289837863559563
Wannan Mutumin dan kasar Oman ya shirya kayan shan ruwa ya ajiye a bakin titi inda yake tare matafiya yana cewa su tsaya su sha ruwa.
Rahotanni sun bayyana cewa, shekarar sa 17 yana wannan abin Alheri.
Inda mutane da yawa suke ta masa fatan Alheri.
https://twitter.com/i/status/2026147800220614756
Dan Fafutuka, Omoyele Sowore ya je Hedikwatar 'yansandan Najeriya dan ya ga sabon IGP saidai 'yansanda da yawa sun ce masa basu ma san an nada sabon IGP din ba.
https://twitter.com/i/status/2026339895707312168
A cewarsu har yanzu Egbetokun ne yake akan kujerar.