Thursday, May 7
Shadow
Ko Buhari Me gidanka ba sau daya ya fito taka ya zama shugaban kasa ba>Masussuka ya gayawa Pantami

Ko Buhari Me gidanka ba sau daya ya fito taka ya zama shugaban kasa ba>Masussuka ya gayawa Pantami

Duk Labarai
Malam Masussuka ya gayawa Hon. Isa Ali Pantami cewa ko Tsohon Shugaban kasa, Muhammadu Buhari me gidansa ba sau daya ya fito takara yayi nasara ba. Yace dan haka shima dan bai samu takarar Gwamnan jihar Gombe ba kamata yayi ya hakura. Masussuka ya kara da cewa, Pantami ya dauka limanci ne saboda yaga da an yi taron manya idan yana gurin ce masa ake ya wuce kawai, to ya sha yanzu ma da ya fito takara haka za'a masa. https://www.tiktok.com/@danmalam807/video/7636889338818710805?_r=1&_t=ZS-969umjqktjF
Nima Ina son Update dina ya fita>>Inji Wannan matashiyar

Nima Ina son Update dina ya fita>>Inji Wannan matashiyar

Duk Labarai
Wata matashiya dake yin Tiktok wadda ke amfani da sunan matar oga ta bayyana cewa, tana son Update dinta itama ya fita. Ta bayyana cewa, dan Namiji ya fitar da Update dinta ko a jikinta babu abinda zata ji. Ta bayyana hakane a yayin da ake kan maganar fitar Bidiyon wata matashiya a Arewa inda ake ta Allah wadai kan lamarin. https://www.tiktok.com/@jamilasani20/video/7636508774890605831?_r=1&_t=ZS-969uBVMHTai
Kalli Bidiyon: Yanda Abokina ya kama Mahaifinsa da kawarsa a Hotel a Zari>>Inji wannan matashi

Kalli Bidiyon: Yanda Abokina ya kama Mahaifinsa da kawarsa a Hotel a Zari>>Inji wannan matashi

Duk Labarai
Matashi me yin sana'ar kasuwancin Forex ya bayyana cewa wani abokinsa ya kama mahaifinsa da kawarsa a dakin Otal a Zaria. Yace sun yi fada da kawar tasa ne ta ce masa zai ga abinda zata masa, kawai sai aka kirashi wani otal yana zuwa sai ya tarar da kawar tasa da mahaifinsa. https://www.tiktok.com/@godbless_mother_forex/video/7636478458499026196?_r=1&_t=ZS-969sr08hiWv
Ɗan majalisa a Borno ya fashe da kuka inda ya roƙi a ba shi dama karo na biyar,ya cewa mutanen mazabarsa shi bawan Allah ne kuma talaka

Ɗan majalisa a Borno ya fashe da kuka inda ya roƙi a ba shi dama karo na biyar,ya cewa mutanen mazabarsa shi bawan Allah ne kuma talaka

Duk Labarai
Ɗan majalisa a Borno ya fashe da kuka inda ya roƙi a ba shi dama karo na biyar. Ɗan majalisar dokokin jihar Borno mai wakiltar mazabar Magumeri, Audu Mustapha Ganga, ya roƙi al’ummarsa da su amince da sake tsayawa takara karo na biyar. Ganga, wanda ya shafe shekaru 16 yana kan kujera, ya fashe da kuka yayin da yake roƙon masu ruwa da tsaki da ke neman a sauya wakilci. A cikin wani bidiyo da ya bazu, ya ce duk da matsin da ya fito daga ciki, ya yi ayyuka da dama ga al’umma, tare da alƙawarin yin ƙarin aiki idan aka sake zaɓensa. Rahotanni sun ce mutum shida sun riga sun sayi fom domin fafatawa da shi a zaɓen. Sai dai wannan roƙo nasa ya jawo muhawara a kafafen sada zumunta, inda wasu ke goyon bayansa, yayin da wasu ke zargin cewa kukan na sa ba gaskiya ba ne. https://...
Ba lallai in iya gudanar da zaben gaskiya ba>>Inji Shugaban INEC, Farfesa Joash Amupitan

Ba lallai in iya gudanar da zaben gaskiya ba>>Inji Shugaban INEC, Farfesa Joash Amupitan

Duk Labarai
Shugaban Hukumar zabe me zaman kanta, Farfesa Joash Amupitan ya bayyana cewa ba lallai a samu zaben gaskiya ba. Ya bayyana cewa dalili kuwa shine saboda matsalolin tsaron da suka mamaye Najeriya. Ya bayyana hakane ranar Laraba a ziyarar da ya kaiwa shugaban 'yansandan Najeriya, IGP Tunji Disu Jihohi daban-daban ne a Najeriya ke fama da matsalolin tsaro wanda suka ki ci suka ki cinyewa
Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya nemi kotu ta bashi damar zuwa Asibiti dan a duba idansa da hakoransa

Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya nemi kotu ta bashi damar zuwa Asibiti dan a duba idansa da hakoransa

Duk Labarai
Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya nemi kotu ta bashi dama ya je a duba lafiyar idansa da ta hakoransa. El-Rufai ya nemi hakan ne a gaban babbar kotun jihar Kaduna inda ICPC ta sake gurfanar dashi dan bayyana sabbin tuhume-tuhumen da take masa. Kotun dai ta amince da wannan bukatar ta malam Nasiru Ahmad El-Rufai inda tace amma Asibitin da za'a dubashi kada ya wuce Abuja. Sannan a tabbatar jami'an ICPC zasu bishi.
Kalli Bidiyon: ICPC ta sake gurfanar da malam Nasiru Ahmad El-Rufai a gaban kotu bisa sabbin zarge-zargen da take masa

Kalli Bidiyon: ICPC ta sake gurfanar da malam Nasiru Ahmad El-Rufai a gaban kotu bisa sabbin zarge-zargen da take masa

Duk Labarai
Hukumar ICPC ta sake gurfanar da tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai a gaban kotu inda take masa sabbin zarge-zarge. ICPC ta kai malam Nasiru Ahmad El-Rufai gaban babbar kotun jihar Kadunane dan Tuhumarsa. Saidai wasu sun rika rade-radin cewa ya rame bayan ganinsa a yau. https://twitter.com/i/status/2051943305517146490