Nasiru ya san matarsa tana kasar Morocco>>Inji Lauyan Khadija
Nasiru dake zargin Sheikh Dr. Ahmad Gumi da rike masa mata.
Yasan cewa matarsa na kasar Morocco, idan yasan cewa tsakaninsa da matarsa suna zaman lafiya kamar yanda yake ikirari, to ya je ya dawo da ita.
Sannan kudin sadakinta ma bai bata ba.
Sannan akwai sanda suka yi fada, ya fitar da ita wajen gidan da suke da kayan bacci a jikinta ya kulle mata kofa ya hanata shiga gida
Sannan ya gaya mata cewa ba zai saketa ko shekara dari za'a yi ana case, zai hana ta gaba ya hanata baya.
Inji Lauyar Khadija Diab 'yar kasar Morocco me suna Bilkisu Abdulrasheed.
https://www.tiktok.com/@rfi_ha/video/7684023040639896852?_r=1&u_code=ejaikd8elj8058&preview_pb=0&sharer_language=en&_d=ejaij098emc1h5&share_item_id=7684023040639896852&source=h5_m×tamp=178911...








