fbpx
Thursday, June 8
Shadow

Auratayya

‘Yan tagwaye sun auri mata daya a Rwanda, sun ce kowa na amfana ba cuta ba cutarwa

‘Yan tagwaye sun auri mata daya a Rwanda, sun ce kowa na amfana ba cuta ba cutarwa

Auratayya
'Yan tagwaye sun auri mata daya a Rwanda, sun ce kowa na amfana ba cuta ba cutarwa. Matar ta bayyana cewa ta fara yin soyayya ne da babban kuma bata taba sanin cewa su tagwaye bane. Kwatsam sai wataran taga kanin nasa ta sumbace shi ya rungume shi, wanda hakan yasa suka fara soyayya. A karshe dai sun aureta duka yanzu tsawon shekaru biyu kenan kuma suna fatan samun karuwa, Sun ce ba ruwansu da sukar da mutanane keyi domin bata damunsu.
So gamon jini: Wata fitacciyar mai amfani da dandanlin Soshiyal midiya musamman (Facebook), Fareeda Tofa, ta ce, a rayuwarta yanzu ba ta da burin da ya wuce taga ta auri Yariman Saudiya, Muhammad Bin Salman.

So gamon jini: Wata fitacciyar mai amfani da dandanlin Soshiyal midiya musamman (Facebook), Fareeda Tofa, ta ce, a rayuwarta yanzu ba ta da burin da ya wuce taga ta auri Yariman Saudiya, Muhammad Bin Salman.

Auratayya
Wata fitacciyar mai amfani da dandanlin Soshiyal midiya musamman (Facebook), Fareeda Tofa, ta ce, a rayuwarta yanzu ba ta da burin da ya wuce taga ta auri Yariman Saudiya, Muhammad Bin Salman. Fareeda Tofa ta bayyana hakan ne yayin zantawa da gidan rediyo Freedom, ta cikin shirin hirarrakin da tashar ke yi da matasa masu amfani Soshiyal midiya. Ta ce, idan Allah ya cika ma ta burinta ta yi “Wuff”! da Yariman na Saudiyya, to za ta tabbatar ya mayar da Najeriya wajen zuwansa a ko da yaushe.
ABIN TAUSAYI: Miji Da Mata Sun Mutu Kwana Biyu Tsakani, Sun Bar Yaransu Kanana Guda Biyu

ABIN TAUSAYI: Miji Da Mata Sun Mutu Kwana Biyu Tsakani, Sun Bar Yaransu Kanana Guda Biyu

Auratayya
ABIN TAUSAYI: Miji Da Mata Sun Mutu Kwana Biyu Tsakani, Sun Bar Yaransu Kanana Guda Biyu Dr Barde Luka Yelwa, wani malamin Kwalejin koyan malanta dake garin Gashua a jihar Yobe ya rasa ransa ranar Alhamis da ya gabata, bayan ya samu bugun zuciya a asibitin da yake jinyar matarsa wacce ba ta da lafiya. Kwana biyu bayan rasuwar mijin nata, ita ma ta rasu a ranar Asabar, inda yau Litinin za a yi jana'izar su biyun a ikkilisiya ta ECWA GOODNEWS dake garin Potiskum a jihar Yobe. Sun mutu sun bar yara biyu, mace yar shekara biyar da kuma namiji dan shekara biyu. Daga Suleiman Dauda