Saturday, March 22
Shadow

A watan Maris matasa masu bautar kasa zasu fara karbar Alawus din Naira dubu 77>>Inji NYSC DG

Hukumar kula da masu bautar kasa a Najeriya, NYSC ta baiwa matasa masu bautar kasar tabbacin cewa, a watan Maris zasu fara ganin karin Alawus zuwa Naira 77,000.

Shugaban hukumar, Brigadier General Olakunle Oluseye Nafiu ne ya bayyana hakan a yayin ganawa da matasan masu bautar kasa a ranar Alhamis.

An yi taron ganawar ne a Wuse da Garki a Abuja.

Brigadier General Nafiu ya bayar da tabbacin cewa Gwamnatin tarayya da Hukumar ta NYSC na kokarin ganin sun jiyawa matasan masu bautar kasa dadi.

Karanta Wannan  Wani gurin Ibada ya bayyana a Legas inda musulmai da kirista ke zuwa suna ibada tare

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *