Tuesday, March 17
Shadow

An kama ‘yan Arewa 89 a Kudu da sunan Wai Mahara ne, saidai ‘yansanda sunce ma’aikatan kamfanin Dangote ne

Wasu ‘yan Arewa 89 da aka kama a Legas da zargin cewa mahara ne, hukumar ‘yansandan Najeriya ta fito tace ba mahara bane, ma’aikatan kamfanin Dangote ne.

Hukumar ‘yansandan Legas sun ce ma’aikatane aka kawo daga Katsina zasu yi aiki a matatar man fetur ta Dangote.

https://twitter.com/ChuksEricE/status/1923264289097281970?t=Ig44GRbIaAHgCrswQluiSg&s=19

Kakakin ‘yansandan jihar Legas, CSP Benjamin Hundeyin ya tabbatar da cewa sun gudanar da bincike kuma sun gano ma’aikatan matatar man Dangote daga Katsina ba mahara ba.

Karanta Wannan  Azabar da 'yan Najeriya ke sha a hannun Tinubu, a yanzu suna rokon Shugaba Buhari ya dawo kan mulki>>Inji Rotimi Amaechi

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *