Monday, December 22
Shadow

Babbar Matsalar Buhari itace yasan da baragirbin Gwamnatinsa amma ya kasa ciresu, ni kaina sai da aka so fitar dani daga Villa amma ba kiya>>A’isha Buhari

Matar tsohon shugaban kasa, Hajiya A’isha Buhari ta bayyana cewa, an so a fitar da ita daga fadar shugaban kasa lokacin mijinta na mulki amma taki yadda.

Tace wani jami’in tsaro ya ce mata ya kamata ta koma Daura da zama saboda suna son yin wani bincike idan an kammala sai ta dawo.

Saidai tace amma taki amincewa da hakan.

A’isha Kuma a cikin Littafin tarihin Rayuwar Buhari da aka rubuta tace babbar matsalar mijin nata yasan bara gurbi a gwamnatinsa amma yaki ciresu daga mukaminsu.

Tace tana fatan Shugaba Tinubu ba zai tafka irin kuskuren da mijin nata a tafka ba.

Karanta Wannan  An samu fargabar dasa Bàm a Jos, Jihar Filato

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *