
Mataimakin gwamnan jihar Bauchi, Auwal Muhammad Jatau ya yi magana akan rahoton dake cewa ya zabgawa ministan harkokin kasashen waje, Yusuf Maitama Tuggar mari.
Jatau yayi magana ta bakin kakakinsa, Muslim Lawal inda yace rahoton marin ba gaskiya bane
Yace su basu ma da labari game da maganar marin a bakin ‘yan jarida suke ji.
Yace babu ta yadda za’a yi mataimakin gwamnan jihar Bauchi ya mari minista, yace ko gwamna ba zai mari minista ba ballantana mataimakinsa.
Kokarin jin ta bakin ministan ya ci tura.