Monday, December 22
Shadow

Da Duminsa: Kasar Amurka tace ta fas kawo Khàrì Najeriya inda tace ta fahimci abinda ke faruwa a Najeriya kuma bai fi karfin jami’an tsaron kasar ba

Rahotanni sun bayyana cewa, kasar Amurka tace ta janye matakin soji da take son dauka akan Najeriya bisa zargin Kisan Kiristoci.

Tace a yanzu bayan ta fahimci yanda abin yake ta gane abune da za’a iya warwareshi ta hanyar diplomasiyya.

Amurkar ta canja matsayine bayan ganawar ‘yan majalisar kasar, Bill Huizenga da Reps. Michael Baumgartner, Keith Self, da Jefferson Shreve, babban me baiwa shugaban kasa shawara kan harkar tsaro Malam Nuhu Ribadu.

Tace ta fahimci akwai banbancin rikicin dake faruwa a Arewa maso gabas da Arewa maso tsakiya.

Tace amma zata ci gaba da aiki da Najeriya wajan ganin lamuran tsaro sun inganta.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyo: An Kama Akwatin Zaɓe Da Na’urar BVAS A Motar Jigon APC, Mustapha Salihu, A Zaben Ganye

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *