Friday, December 26
Shadow

Da Duminsa: Wasu sojojin Najeriya sun Shirya yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu juyin Mulki saidai an yi nasarar kamasu kamin su ida nufinsu

Rahotanni daga kafar Sahara reporters wanda tace ta samo ta wasu majiyoyi sun ce wasu sojoji sun yi yunkurin yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu juyin Mulki.

Sojojin sun shirya juyin Mulkinne ranar 1 ga watan Oktoba ta hanyar harbe shugaban kasar da wasu manyan jami’an tsaronsa sannan su ayyana gwamnatin Soja.

Rahoton yace sojoji 16 yanzu haka suna hannu wadanda suka fara daga mukamin Kaftin zuwa Brigadier General bisa wannan zargi.

Sahara reporters tace hukumar sojin tace an kama sojojin ne bisa laifuka daban-daban da suka aikata amma ba haka bane gaskiyar lamarin.

Majiyar tace an ce sun aikata wasu laifukane kawai dan ba’a so maganar ta fita.

Karanta Wannan  Bayan da suka ta yi yawa, Ministan Abuja, Nyesom Wike yace baya dana sanin Sakawa babban dakin Taron Najeriya sunan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *