Friday, January 16
Shadow

Daga yanzu sai limamai sun rika gabatar da Hudubar Juma’a an tantance bata sabawa tsarin Gwamnati ba kamin a amince su hau Munbari su yi ta>>Inji Gwamnan jihar Naija, Umar Bago

Gwamnan jihar Naija, Umar Bago ya bayyana cewa, daga yanzu sai an tantance hudubar Juma’a kamin a yadda limami ya hau Mumbari ya gabatar da ita.

Gwamnan ya tabbatar da hakan ne a hirar da aka yi dashi a hidan Talabijin na TVC ranar Lahadi.

Yace ba zasu amince da a rika yada hudubar data zama zata cutar da mutane ko gwamnati ba.

Gwamnan ya kara da cewa, suna aiki da hukumomin tsaro dan tabbatar da faruwar hakan.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyon yanda Gwamna Abba Kabir Yusuf ya fito ya gaisa da masoyansa da suka je tayashi murnar sabuwar shekara a daren jiya

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *