Monday, March 17
Shadow

Dalla-Dalla: Sanata Natasha Akpoti ta fitar da kalaman batsa da Sanata Godswill Akpabio ya gaya mata bayan da ta je ofishinsa

Sanata Natasha Akpoti daga jihar Kogi ta bayyana kalaman batsa da Sanata Godswill Akpabio ya gaya mata bayan da ta je ofishinsa.

Tace ta je ofishinsa ne dan jin ba’asin abinda yasa ba’a amincewa da kudirorin dokar da take kawowa majalisar inda ta bayyana cewa, kudirorin na da matukar muhimmanci a wajan jama’ar mazabarta.

Tace tana mai magana kawai sai yace mata idan tana son kudirorin data kawo su wuce to sai ta yadda ta jiya masa dadi.

Tace sai ta yi kamar bata ji ahinda yace ba ta ci gaba da maganarta, tace amma ya sake gaya mata cewa, zabi ya rage nata.

Karanta Wannan  Ya kamata Gwamnonin Arewa su canja matsaya akan kin amincewa da kudirin dokar Haraji da Shugaba Tinubu ya kawo,abu ne me kyau da zai karawa gwamnati hanyar kudaden shiga>>Inji Sanata Shehu Sani

Sanata Akpoti ta bayyana hakane a hirar da aka yi da ita a gidan talabijin na Arise TV inda ta zargi Sanata Akpabio da neman yin lalata da ita.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *