Tuesday, March 17
Shadow

Dangote ya bayar da lambar waya yace a kai masa rahoton duk wani gidan man MRS dake sayar da man fetur sama da Naira 739 akan kowace lita

Matatar man fetur ta Dangote ta bukaci ‘yan Najeriya dasu saka ido akan duk gidan man MRS dake sayar da man fetur sama da Naira 739 akan kowace lita su kai kararshi.

Sanarwar tace matatar man Dangote tuni ta fara sayar da man akan wannan farashin ta hanyar gidajen man MRS dake fadin kasarnan.

Sannan za’a samar da wadataccen man dan kaucewa wahalar man da ake yawan fuskanta kusan duk karshen shekara.

Sanarwar ta bayar da lambar wayar da za’a kira dan kai korafin kamar haka: 0800 123 5264

Karanta Wannan  Kalli Bidiyon yansa Lauyoyin Nnamdy Khanu suka je ofishin DSS dan ganinshi amma aka ce musu an mayar dashi Gidan Gyaran Hali dake Sokoto

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *