Friday, May 23
Shadow

Duk wanda yace ban yi komai ba tun bayan hawa Mulkin Najeriya Makahone kuma Kurmane>>Shugaba Tinubu

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, duk wanda ke ikirarin bai aikata komai ba bayan hawa mulki to Makahone kuma kurma ne.

Shugaban ya bayyana hakane ta bakin me magana da yawunsa, Daniel Bwala.

Ya bayyana hakanne a hirar da aka yi dashi a TVC News inda yace shugaba Tinubu ya kara yawan kudaden da Najeriya ke ajiye dasu a bankin Amurka inda kuma ya biya tarin bashin da tsohuwar gwamnatin da ya gada ta bar masa.

Ya kara da cewa kuma Shugaba Tinubu ya kara yawan kudaden da yake aikawa jihohi, yace kamin zuwan Tinubu jihohi 27 sun Talauce basa iya biyan Albashi.

Karanta Wannan  Innalil-Lahi wa'inna iLaihi rajiun: Allah ya yiwa dalibai almajirai (17) Rasuwa Agarin Kauran-Namoda sanadiyyar Gobara wadda ta shafe awa uku tana ci

Yace amma a yau babu jihar da ta Talauce ko ta kasa biyan Albashi.

Yace ba biyan Albashi ba kadai yanzu Jihohi na gudanar da ayyukan ci gaba inda yace kwanannan suka je jihar Katsina, kuma Gwamnan jihar ya tabbatar da wannan magana ta cewa a baya akwai gwamnonin da basa iya biyan Albashi.

Ya kuma ce akwai bashin karatu wanda a yanzu ‘ya’yan Talakawa na iya zuwa su nema dan su yi karatu.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *