Friday, January 16
Shadow

Gajartace tawa El-Rufai yawa shiyasa ya ke ta soki burutsu>>Inji Shugaba Tinubu

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, gajarta ce tawa tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai yawa shiyasa yake ta soki burutsu.

Ya bayyana hakane ta bakin kakakinsa, Bayo Onanuga.

El-Rufai a wata hira da aka yi dashi yace a wata kuri’ar jin ra’ayin jama’a da suka gudanar sun gano cewa, Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ba zai ci zaben shekarar 2027 ba.

Saidai Onanuga yace babbar matsalar El-Rufai shine shi a ko da yaushe yana son ya nuna yafi sauran mutane.

Yace El-Rufai bashi da biyayya inda yawa mutane da yawa a baya ciki hadda wansa wanda tsohon soja ne.

Karanta Wannan  Matukar Muneerat Abdulsalam Ta Amince Ta Zo Mu Yi Aure, Dama Ina Da Burin Auren Wadda Ta Girme Ni, Inji Malam Musa Rafin Kuka

Yace kuma makaryaci ne sosai wanda ke yin abubuwa yawanci dan kawai amfanin kansa.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *