Friday, December 5
Shadow

Gwamnan Jihar Kano Ya Ayyana Ranar Litinin A Matsayin Ranar Hutu Saboda Ràśuwar ’Yan Wasan Kwallon Kafa Na Kano Pillars

Gwamnan jihar Kano dake arewacin Najeriya Abba Kabir Yusuf, ya ayyana Litinin, 2 ga Yuni, a matsayin ranar hutu domin bawa al’umma su yi addu’a da jimamin ƴan wasan jihar 22 da suka rasu a hatsarin Mota ranar Asabar.

Gwamnan ya kuma bayyan alhini tare da miƙa saƙon ta’aziyya ga iyalan mamatan.

Wannan na ƙunshe ne ta cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Asabar 31 ga Mayu, 2025.

Haka kuma gwamna Abba ya bukaci limamai da ɗaukacin musulmi dake gida da na ƙasa mai tsarki da suka je aikin hajji su yi addu’ar neman rahama ga mamatan da kuma juriya ga iyalansu.

Karanta Wannan  Saudiyya ta ayyana ranar da masu aikin Umrah za su fice daga kasar

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *