Saturday, March 15
Shadow

Har yanzu Hukumar HISBAH ta Kano ta kasa kwato Shafinta na Facebook da aka mata kutse ana ta saka hotunan batsa

Shafin Facebook na hukumar HISBAH ta Kano har yanzu yana hannun wani bata gari da ya musu kutse kuma yace saka hotunan batsa a kansa.

Tun a watan Augusta na shekarar 2024 ne dai aka yiwa shafin kutse inda Hukumar HISBAH din ta rasa iko dashi, yanzu watanni 6 kenan.

Shugaban HISBAH, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya tabbatar da faruwar lamarin inda yace bangaren fasahar zamani na HISBAH suna kan kokarin dawo da shafin hannun hukumar.

Saidai har yanzu shiru kake ji.

Da Sahara Reporters suka tuntubi hukumar ta HISBAH tace har yanzu tana kan kokarin kwato shafin daga hannun bata garin da suke da iko dashi.

Karanta Wannan  Sabon Shugaban Hukumar Kula Da Gidan Yari Na Jihar Katsina Ya Ziyarci Buhari Bayan Ya Karbi Ragamar Kama Aiki

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *