Friday, December 26
Shadow

Ina da yakinin Amaechi da matarsa Barayi ne, kuma idan aka bincikesu ba’a gano kudin sata ba, zan sauka daga mukamin ministan Abuja>>Inji Wike

{“remix_data”:[],”remix_entry_point”:”challenges”,”source_tags”:[],”origin”:”unknown”,”total_draw_time”:0,”total_draw_actions”:0,”layers_used”:0,”brushes_used”:0,”photos_added”:0,”total_editor_actions”:{},”tools_used”:{},”is_sticker”:false,”edited_since_last_sticker_save”:false,”containsFTESticker”:false}

Ministan babban birnin tarayya, Abuja, Nyesom Wike ya bayyana cewa, idan aka binciki Tsohon Ministan sufuri, Rotimi Amaechi da matarsa akan kudaden hukumar NDDC ba’a samesu da laifi ba, zai sauka daga Ministan Abuja.

Wike ya roki shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da ya saki rahotan binciken hukumar wadda ta raya yankin Naija Deltace.

Wike ya fadi hakane a hirar da aka yi dashi a gidan Talabijin na Channels TV inda yake mayar da martani kan zargin da Amaechi ya masa cewa, shi dan rashawa ne.

Wike yace NDDC ta rika baiwa matar Amaechi Naira Biliyan 4 da sunan zata baiwa mata horo duk wata.

Karanta Wannan  YANZU YANZUHukumar EFCC zata binciki ƙaramin ministan tsaro, Bello Matawalle, akan zargin wawure Naira biliyan 528

Yace dan haka yake rokon shugaba Tinubu ya taimaki ‘yan Najeriya tmya wallafa sakamakon binciken da aka gudanar.

Wike yace ko a makaranta Amaechi dakiki ne.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *