Friday, December 5
Shadow

Inada masaniya kan Inda ake tsare da ‘yan mata ‘yan makaranta na jihar Kebbi>>Inji Sanata Garba Maidoki

Sanata Garba MaiDoki daga jihar Kebbi ya bayyana cewa suna da masaniya kan inda ‘yan Bindiga suka boye ‘yan mata ‘yan makaranta da suka sace.

Ya bayyana hakane a wata ganawa da aka yi dashi a Channels TV inda yace ba’a fita da ‘yan matan daga yankin Kebbi ta kudu ba.

Ya kuma bayar da tabbacin nan da kwanaki 1 zuwa 2 za’a dawo da ‘yan matan.

‘Yan mata ‘yan makaranta su 25 ne dai aka sace daga Maga jihar Kebbi.

Karanta Wannan  Ji yanda Naira Tiriliyan 210 ta yi batan dabo a kamfanin mai na kasa, NNPCL

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *