BABBAR MAGANA: Tun Cikin Azumi Aka Yi Zaton Ța Mùtu Sai Gashi Ta Dawò Gida, Ashe Ba Ita Ta Mùťù Bà.

Billahillazi yanzu a daren nan aka kawo min wani labari a cikin garin Kura dake Kano Wallahi Tallahi wai wata yarinya ce Allah Ya yi mata rasuwa tun a cikin azumi sai yau aka ganta kawai ta dawo gida luma Wallahi ita ce.
Ni ma ina zaune ina cin abinci aka zo ana fada min ban yadda ban gama cin abincin ba na tashi na je domin na gani da idona. Wallahi ina zuwa har unguwar tasu kawai na ga kofar gidan su yarinyar cike da mutane na ta shiga ana ganinta.
Ni ma na ganta Wallahi abun dai akwai mamaki sosai. Abu kamar a fim mutum ya mutu amma ya dawo.
Adreshin unguwar da yarinyar take Alkalawa ne a cikin garin Kura dake Kano.
Amma dai abun akwai mamaki sosai Wallahi. Ikon Allah. Allah Ka sa dai mu dace kawai.
Saidai daga bisani wata majiya ta gitar da gaskiyar abinda ya faru game da yarinya da aka ce ta bayyana bayan ta rasu.
Ita wannan baiwar Allah da azumi ta bata ba a ganta ba sai daga baya aka samu labarin wai ta mutu.
An tsinci gawarta har an binne ta sai yau kuma a ka ganta. Bincike ya nuna cewa gawar da aka binne ba tatabbatacce bane kawai an fadawa iyayen ta ne an binne ta, domin da kaya ta dawo gida ba likkafani ba. Sannan babu tabbacin ita aka binne.
Daga Corm Usama Lere Kura