Monday, March 16
Shadow

Jihohin Katsina da Bauchi sun bayar da hutun Azumin Watan Ramadan ga ‘yan makaranta

Jihohin Bauchi da Katsina sun bayar da hutun Watan Azumin Ramadana ga ‘yan makaranta.

A jihar katsina, bayan kulle makarantun Gwamnati, Hukumar HISBAH ta jihar ta kuma fitar da sanarwa ga masu marantu masu zaman kansu dasu kulle makarantun nasu har sai bayan Azumin watan Ramadana.

Kwamandan HISBAH na jihar, Aminu Usman ne ya fitar da sanarwar inda yace rashin yiwa wannan doka biyayya zai sa a hukunta duk makarantar da aka kama suna karatu.

Hakanan a jihar Bauchi na, mahukuntan jihar sun bayar da hutu daga ranar 26 ga watan Fabrairu zuwa ranar 5 ga watan Afrilu ga makarantu.

Karanta Wannan  Duk da akwai wahala amma sai Gwamnati ta ci gaba da tsarin da take kai a yanzu na tsawon shekaru 15 kamin Najeriya ta ci gaba>>Bankin Duniya

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *