Tuesday, March 17
Shadow

Jirgin ƙasa daga Abuja zuwa Kaduna ya sauka daga kan layin dogo

Jirgin ƙasa ɗauke da fasinja da ya taso daga Abuja babban birnin Najeriya zuwa Kaduna ya faɗi a ranar Talata da safe.

Lamarin dai ya jefa fargaba a tsakanin fasinjoji da ke cikin jirgin.

Rahotanni na cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 11 na safe a kauyen Asham da ke hanyar Abuja zuwa Kaduna kuma jirgin ƙasa ta bar Abuja ne da misalin karfe 9:45.

Har yanzu ba a san abin da ya jawo saukar jirgin daga kan layin dogo ba, kuma babu tabbacin ko an samu waɗanda suka jikkata.

Hukumar Jiragin ƙasar Najeriya (NRC) bata yi tsokaci ba a kan lamarin.

Karanta Wannan  Goodluck Jonathan, da Bukola Saraki sun yiwa Tsohon Shugaban kasa, Marigayi Umar Musa 'Yaradua addu'a

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *