Friday, December 26
Shadow

Ka bude iyakoki a kaiwa Falasdiynawa Tallafin kayan Abinci>>Donald Trump ya gayawa Benjamin Netanyahu

Shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya bayyanawa shugaban kasar Israela, Benjamin Netanyahu cewa a bide iyakokin kasar Falasdinawa a kai musu agajin kayan abinci da sauran kayan Masarufi.

Ya bayyana hakanne a wata ganawa da suka yi ta wayar salula.

Trump yace Falasdinawa na cikin halin matsin rayuwa kuma ya kamata a kyautata musu.

Masu sharhi akan al’amuran yau da kullun sun bayyana cewa, wannan magana ba lallai tawa Benjamin Netanyahu dadi bane.

Hakanan a wani yanayi da ake kallon na mayar da Benjamin Netanyahu gefe, Trump yayi sulhu da mayakan kasar Yemen, sannan ya ci gaba da tattaunawa da kasar Iran kan makamashin kare danginta.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyon: Akwai aya a Qur'ani da idan ka karanta ta zaka bace, Lokacin ina yaro nasha Karanta ta idan na yi lattin zuwa makaranta kuma ba'a ganina>>Inji Wannan malamin Addinin Islaman daga yankin Yarbawa

Hakanan Wani rahoto yace Trump ya nuna cewa baya bukatar Netanyahu wajan mu’amala da Gabas ta tsakiya.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *