Friday, December 5
Shadow

Kalli Bidiyo: An zargi Ana yiwa kananan yara maza fyade a gidan yarin Goron Dutse dake Kano

Wani faifan Bidiyo ya bayyana inda aka ji wani bawan Allah na ikirarin cewa ana yiwa yara maza fyade a gidan yarin Goron Dutse dake Kano.

Yace ana amfani da kananan shekaru da yaran ke da su da kuma bukata ta abinci da suke da ita ana lalata dasu.

Yace a wasu lokutan ma ana hada baki da wasu bata garin ma’aikatan gidan yarin ana basu kudi ana baiwa yaran a daukesu, yace a wasu lokutan kuma yawan kudin da za’a baiwa yaranne ke daukar hankalinsu su aikata wannan masha’a.

https://twitter.com/bapphah/status/1918931313190412518?t=Ul1rceH1xKpQnZ_oIIHdpQ&s=19

Yace yana kira ga hukumomi da su je su bincika abubuwan da ya fada inda yace akwai ma abubuwan da bai fada ba wanda ake yi a gidan yarin.

Karanta Wannan  Tonon Silili, Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo ya haura shekaru 90 ba 88 kamar yanda yake ikirari>>Inji Tsohon Gwamnan Ogun, Amosun

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *