
A daren da ya gabata ne dai aka samu tashin Gobara a kasuwar Taminus ta garin Jos na jihar Filato.
Daya daga cikin abinda mutane da yawa ke kokawa akai shine yanda jami’an kashe Gobara basu kai musu dauki da wuri ba.
Hakanan an koka kan yanda jami’an tsaro suke korar mutane daga wajan gobarar.
Wani Bidiyo da ya watsu sosai a kafafen sada zumunta an ji wasu na zargin cewa akwai hannun gwamnati a lamarin.