Wednesday, May 7
Shadow

Kalli Bidiyon mummunar girgizar kasar data faru a kasar Turkiyya, mutane na ta gudun ceton rai

Aƙalla mutane 151 ne suka samu raunuka bayan sun durgo daga dogayen gine-gine saboda tsoron da girgizar ƙasa ta haifar, a cewar ofishin gwamnan Istanbul.

https://www.tiktok.com/@live_news00/video/7496509730362281238?_t=ZM-8vmJNkmOYiL&_r=1

Ofishin ya kuma wallafa a shafinsa na X, cewa ba a samu asarar rayuka ba, kuma babu wani gini da mutane ke zaune a ciki da ya ruguje.

Sai dai wani gini wanda babu kowa a ciki ya ruguje sakamakon girgizar ƙasar.

Ministan ilimi na Turkiyya, Yusuf Tekin ya sanar da cewa za a rufe makarantu na kwana biyu Alhamis da Juma’a.

Karanta Wannan  Dalilin da yasa na kifar da gwamnatin Buhari duk da yake cewa nine shugaban ma'aikatansa>>IBB ya magantu

Aƙalla an samu girgiza sau 51 a birnin a ranar Laraba, inda mafi girmansu ya kai ƙarfin maki 6.2, wanda ya shafi Istambul tun da fari, a cewar ministan cikin gida, Ali Yerlikaya.

Tuni masana kimiyya sun ce babbar girgizar ƙasa za ta iya afkawa birnin a kowane lokaci, hakan ya sa a abin da ke faruwa a yanzu ya sanya fargaba a cikin zukatan mazauna birnin.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *