Saturday, December 13
Shadow

Kalli Bidiyon mummunar girgizar kasar data faru a kasar Turkiyya, mutane na ta gudun ceton rai

Aƙalla mutane 151 ne suka samu raunuka bayan sun durgo daga dogayen gine-gine saboda tsoron da girgizar ƙasa ta haifar, a cewar ofishin gwamnan Istanbul.

https://www.tiktok.com/@live_news00/video/7496509730362281238?_t=ZM-8vmJNkmOYiL&_r=1

Ofishin ya kuma wallafa a shafinsa na X, cewa ba a samu asarar rayuka ba, kuma babu wani gini da mutane ke zaune a ciki da ya ruguje.

Sai dai wani gini wanda babu kowa a ciki ya ruguje sakamakon girgizar ƙasar.

Ministan ilimi na Turkiyya, Yusuf Tekin ya sanar da cewa za a rufe makarantu na kwana biyu Alhamis da Juma’a.

Karanta Wannan  Ni na yi imani, Waka halalce kuma wakar da nake yi zata kaini Alhannah, amma duk randa na gane waka Haramun zan daina yi>>Inji Ali Jita

Aƙalla an samu girgiza sau 51 a birnin a ranar Laraba, inda mafi girmansu ya kai ƙarfin maki 6.2, wanda ya shafi Istambul tun da fari, a cewar ministan cikin gida, Ali Yerlikaya.

Tuni masana kimiyya sun ce babbar girgizar ƙasa za ta iya afkawa birnin a kowane lokaci, hakan ya sa a abin da ke faruwa a yanzu ya sanya fargaba a cikin zukatan mazauna birnin.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *