
Dr. Hussain ya mayarwa da Baffa Hotoro raddi kan sukar da Baffa Hotoron yayi game da kalaman Dr. Hussain na cewa yana rokon Allah kada ya kai matsayin da sai Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ceceshi ranar tashin qiyama kamin ya shiga Aljannah.
Dr. Hussain a wani Bidiyo daya yadu sosai a kafafen sada zumunta yayi ta Zhaghin Baffa Hotoro inda yace shi da ya kasa hana matarsa yin bikin Birthday shine yake tunanin zai hanashi yin da’awa?
Baffa Hotoro dai ya baiwa Dr. Hussain shawarar ya koma makaranta inda yace kalaman na Dr. Hussain jahilci ne.