
Mutanen garin Abeokuta jihar Ogun sun tashi da wani abin mamaki inda aka ga gawar wata mata akan titin OGTV.
An gano cewa bayan kasheta an kuma yanke mata al’aura.
Lamarin ya farune ranar Talata inda tuni aka kaiwa ‘yansanda korafi.
Ba’a dai gano wanda suka yi wannan aika-aika ba amma an yi amannar cewa tsafi ne suke son yi musamman da al’aurarta da suka cire.
Tuni aka kai gawarta Mutuware.