Friday, December 5
Shadow

Kalli yanda aka kama wasu na cinikin sassan jìkìn mutane

‘Yansanda a jihar Ogun a karkashun rundunarsu ta SWAT sun kama wasu mutane da ake zargin suna safarar sassan jikin mutane.

Da farko dai an kama Sunday Akintobi dan kimanin shekaru 36 a Itoku ta garin Abeokuta inda daga baya kuma aka kama karin mutane 2 Oladimeji Olaniran dan shekaru 40 da kuma Isaiah Tijani dan shekaru 38.

Kakakin ‘yansandan jihar, CSP Omolola Odutola, ya tabbatar da faruwar lamarin inda yace an gano wasu abubuwa a gidajen wadannan mutane wanda an yi amannar cewa sassan jikin mutanene.

Yace kwamishinan ‘yansandan jihar ya bayar da umarnin yi bincike kan lamarin.

Karanta Wannan  Matashin Dan Kwallon Nijeriya Kenan, Anas Yusuf Mai Shekaru 21, Wanda Yanzu Haka Suke Wakiltar Nijeriya A Gasar CHAN 2025

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *