Tuesday, February 3
Shadow

Kalli yanda aka kama wasu na cinikin sassan jìkìn mutane

‘Yansanda a jihar Ogun a karkashun rundunarsu ta SWAT sun kama wasu mutane da ake zargin suna safarar sassan jikin mutane.

Da farko dai an kama Sunday Akintobi dan kimanin shekaru 36 a Itoku ta garin Abeokuta inda daga baya kuma aka kama karin mutane 2 Oladimeji Olaniran dan shekaru 40 da kuma Isaiah Tijani dan shekaru 38.

Kakakin ‘yansandan jihar, CSP Omolola Odutola, ya tabbatar da faruwar lamarin inda yace an gano wasu abubuwa a gidajen wadannan mutane wanda an yi amannar cewa sassan jikin mutanene.

Yace kwamishinan ‘yansandan jihar ya bayar da umarnin yi bincike kan lamarin.

Karanta Wannan  Bankin China ya bai wa Najeriya rancen kuɗin gina titin jirgi kasa daga Kano zuwa Kaduna

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *