
Daga Auwal Isa Musa
Kamar yadda wakilin Jaridar Taskar Labarai taskar labarai ya aiko mana, cincirindon jama’a ne suka yi farin-dango wajen fitowa tare da bazama a kan manyan Titunan birnin Katsina da hantsin yau Asabar, domin gudanar da zanga-zanga maintaken “Takalmin Annabi ya fi kowa”
Bangarorin al’ummar musulmi a jihar ta katsina, an shaida shigarsu wannan zanga-zanga wadda yanzu haka take gudana a tsanake, a yain da mahalartanta ke rera wakokin yabo ga fiyayyen halitta, musamman Takalminsa (S) da suka fito zanga-zangar nuna daraja da fifikonsa.
Zanga-zangar ta taso ne taso ne daga filin Polo/kofar ‘yandaka, inda ta ta nufo cikin gari.