Friday, December 5
Shadow

Kasar mu kasa ce me cin gashin kanta dan haka bamu amince da duk wani sharadi da kasar Amurka ta gindaya na hanamu ci gaba da kokarin mallakar makamin Kare dangi ba>>Inji Ìràn

Kasar Iran ta mayar da martani kan sharadin da kasar Amurka ta sanya mata na tattaunawar sulhu da suke kan shirinta na mallakar makamin kare dangi.

Rahotanni sun bayyana cewa, Amurka ta ce Iran zata iya ci gaba da inganta makamashin kare dangi amma a hankali ba da gaggawa kamar yanda take yi a yanzu ba.

Saidai Iran tace ita kasa ce me cin gashin kanta dan haka bata amince da sharadin da Amurka ta gindaya mata ba.

A baya dai hukumar kula da makamashin Nokiliya ta Duniya ta bayyana cewa, Iran ta inganta makamashin Uraniyum zuwa matakin kaso 60 cikin 100 wanda gaf take da ta kai matakin kaso 90 cikin 100 wanda shine zai bata damar mallakar makamashin kare dangi.

Karanta Wannan  Kamfanin mai na kasa, NNPCL ya rage farashin man fetur a Abuja da Legas kadai

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *