Wednesday, April 8
Shadow

Kasar Pakistan ta bayyana goyon baya ga Ìràn

Kasar Pakistan ta bayyana cewa, tana goyon bayan kasar Iran a ci gaba da gumurzun da suke da kasar Israyla.

Pakistan ta yi Allah wadai da hare-haren da kasar ta Israyla ta kaiwa Iran inda a wasu rahotannin ta bayyana cewa, a shirye take ta goyi bayan Iran a wannan rikici.

A jiyane dai yaki ya barke tsakanin Israyla da Iran inda Israyla ta fara kaiwa Iran hari inda ta kashe manyan sojojinta da dayawa daga cikin masana kimiyyar ta.

Kasar dai ta zargi Iran da yunkurin mallakar makamin Kare dangi wanda tace ba zata amince da hakan ba.

Israyla ta kaiwa Iran hare-hare akan tashar inganta makamin kare danginta.

Karanta Wannan  Jihar Enugu tace zata rage farashin wutar Lantarki wa mutanen jiharta saboda kudin sun yi yawa, saidai kamfanin wutar Lantarki na kasa yace jihar dama duk wata jiha basu isa su rage kudin wutar ba

Saidai daga baya itama iran ta yi ramuwar gayya.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *