Friday, December 5
Shadow

Kasashen Larabawa sun yi Allah wadai da kasar Israyla saboda hanasu kaiwa Falasdiynawa ziyara da ta yi

Ministocin harkokin wajen ƙasashen Larabawa sun bayyana rashin jin daɗinsu ga gwamnatin Isra’ila, game da rashin amincewa da tawagar ƙungiyar ƙasashen ta ziyarci yankin da aka mamaye a Gaɓar Yamma da kogin Jordan don tattaunawa da shugaban Falasɗinawa.

A wani taron manema labarai, ministan harkokin wajen Saudiyya, Yarima Faisal bin Farhan Al Sa’ud, ya ce matakin da Isra’ila ta ɗauka kamar watsi ne da tayin zaman lafiya.

A ranar Asabar wani jami’in Isra’ila ya ce batun samar da ƙasar Falasɗinu ne manufar ziyarar.

Cikin wata sanarwar haɗin-gwiwa, ƙasashen Masar da Qatar sun ce za su ruɓanya ƙoƙarinsu don a cimma yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza.

Karanta Wannan  Da Duminsa: Kungiyar Gwamnonin Najeriya tace bata yadda shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya kara harajin VAT ba

Shugaban ƙungiyar ƙasashen Larabawa da ministoci huɗu sun gana da shugaban Falasɗinawa Mahmoud Abbas ta kafar Intanet.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *