Friday, December 5
Shadow

Kaso 85 na wadanda muke daukar nauyinsu mu aikasu karatu kasashen Turawa basa dawowa dan su taimaka a gina kasarnan>>Gwamnatin Tarayya ta koka

Gwamnatin tarayya ta koka da cewa, Kaso 85 na daliban Najeriya da take daukar nauyinsu dan zuwa kasashen waje su karo ilimi da zummar su dawo dan ciyar da Najeriya gaba, basa dawowa.

Ministan Ilimi, Dr Tunji Alausa ne ya bayyana hakan a wajan wani taro da ya wakana a Legas.

Yace dalilin haka yasa suka canja lissafi domin sun gano cewa yawanci karatun da ake daukar nauyin daliban su je su yi a kasashen da suka ci gaba, za’a iya yinsa a Najeriya.

Yace dan hakane suka mayar da hankali wajan karfafa harkar ilimin a Najeriya inda yace sun bude cibiyoyin bincike da zurfafa ilimi a jami’o’i daban-daban na kasarnan.

Karanta Wannan  Bidiyo Da Duminsa: Kasar India ta Jefawa kasar Pakistan makami inda ya kàshè karamin yaro da jikkata mutane 2

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *