Saturday, May 10
Shadow

Ko Tinubu mutumin kirki ne ko Mugune sai ya sake zama shugaban kasa a shekarar 2027 yayi 8 kamin ya sauka>>Inji Gwamnan Nasarawa, Abdullahi Sule

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya baiwa ‘yan Arewa baki inda yace su yi hakuri da gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad su koma goyi bayanshi ya sake zama shugaban kasa a shekarar 2027.

Ya bayyana hakane jiya a wajan wani taro da aka yi a Akwanga dake jihar inda yace ko Tinubu mutumin kirkine ko Mugune sai ya kammala mulkin shekara 8 kamin ya sauka.

Yace Arewa ta yi mulki na shekaru 8 dan haka suma kudu sai sun yi mulkin shekaru 8 kamin mulkin ya dawo Arewa.

Yace ‘yan siyasane kawai suke kawo rudani saboda basu samu abinda suke so ba.

Yace a baya wasu gwamnoni sun rika gaya musu cewa Tinubu ne zabin shugaban kasa dan zai gyara Najeriya kamar yanda ya gyara Legas.

Karanta Wannan  Masoya Aminu Ado Bayero sun yi Sallar Rokon Allah ya dawo dashi kan sarautar Kano

Yace amma yanzu sai a canja magana?Yace maganar gaskiya sai Tinubu yayi Takwas.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *