Friday, December 5
Shadow

Ku bi duk inda masu yiwa Najeriya barazanar tsaro suke ku gama dasu>>Shugaban Sojojin Najeriya ya baiwa sojojin Umarni

Shugaban sojojin Najeriya, COAS, Lt.-Gen. Olufemi Oluyede ya baiwa sojojin Umarnin su bi duk inda masu yiwa Najeriya barazanar tsaro suke su gama dasu.

Ya bayar da wannan umarnin ne a yayin bikin sallah tare da sojojin a Giwa dake jihar Kaduna.

Maj.-Gen. Erema Akerejola, ne ya wakilci shugaban sojojin a wajan bikin sallar.

Yace biyayya da karfin hali da sojojin Najeriya ke nunawa ya taimaka matuka wajan nasarorin sa suke samu a fagen daga.

Ya kuma jinjinawa sojojin da suka rasa rayukansu a fagen daga inda yace yana baiwa iyalansu tabbacin jajircewar da suka nuna ba zata tafi a banza ba.

Karanta Wannan  Dan Arewa dake zaune a kudancin Najeriya ya tsinci wayar iPhone 13 promax ya mayarwa me ita

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *