Wednesday, March 18
Shadow

Kuma Dai: Bayan X, Hukumar DSS ta kuma aikawa Facebook bukatar kulle shafin Sowore

Hukumar ‘yansandan farin kaya, DSS ta aikawa da kamfanin Meta me mallakar Facebook da bukatar kulle shafin mawallafin jaridar Sahara Reporters kuma me ikirarin kare hakkin bil’adama, Omoyele Sowore.

DSS kamar yanda suka aikawa X sun bukaci cewa, Facebook su kulle shafin Sowore saboda sakon da ya wallafa me cewa shugaban kasa me laifine sannan kuma ya yi karya a Brazil inda yace ya magance matsalar rashawa da cin hanci amma a zahiri bai magance din ba.

DSS kamar yanda suka gayawa X sun ce wannan sakon ya kawo matsalar tsaro da cin zarafi ga shugaban kasa da sauransu.

Saidai Sowore duk da wannan bai nuna alamar nadama ba.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyo: Dansandan Najeriya ya koka da bashi Naira Miliyan 2.8 a matsayin kudin sallama bayan kammala aikin da ya shafe tsawon shekaru 35 yana yi, yace wannan rashin adalci be ba zai karbaba

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *