Friday, May 30
Shadow

Mun gano cewa El-Rufai na kokarin Tadewa Tinubu kafa ya hanashi zarcewa a 2027, saidai abin da ke mana dadi ‘yan Arewa basu tare ashi>>APC

Jam’iyyar APC ta mayar da martani akan maganganu da avubuwan da tsohon gwamnan jihar Kaduna Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ke yi.

Kakakin APC, Ajibola Basiru ne ya bayyana hakan a wata ganawa da yayi da manema labarai inda yace abinda ke damun El-Rufai shine da bai samu ya zama minista a Gwamnatin Tinubu ba.

Yace daga nan ne sai El-Rufai ya koma sukar Gwamnatin Tinubun, yace amma abinda ke musu dadi shine a Arewar ma shi ba wani me fada aji bane.

Ya kara da cewa, El-Rufai na ta kokari ne kawai yaga ya kawo tarzoma da raba kai tsakanin Arewa da kudu, ta wannan hanyar ne yake son yin suna.

Karanta Wannan  Ku daina Rige-Rigen zuwa kasashen waje neman aiki, Ku tsaya mu gyara kasa>>Shugaba Tinibu ya roki Matasa

Tsohon Gwamnan na Kaduna dai sunansa ya fito a cikin mutanen da Tinubu yaso ya nada a matsayin ministoci amma da yaje majalisa sai ya kasa tsallake tantancewar da aka yi kokarin yi masa.

bayan nan an ga El-Rufai ya je yana ta bibiyar tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar wanda a baya ana ganin dangantaka tsakaninsu ta yi tsami. Ko da gaisuwar mutuwar Edwin Clark, El-Rufai tare suka je da Atiku inda kuma suka je suka yi sallar Juma’a tare.

Hakanan a Kaduna ma an ga yanda El-Rufai ya gana da wakilan Jam’iyyar PDP wanda ake tsammanin ko zai koma Jam’iyyar ne.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *