
A jihar Kano, hukumar Hisba ta sanar da cewa ta warware korafe-korafe ko rigingimu tsakanin ma’aurata har dari shida da ashirin da daya cikin shekara daya.
Mutuwar aure gagarumar matsala ce da ke shafar mutane, kama daga matan da ake saki da mazan da ‘ya’yan, sanadiyyar wani sabani ko rashin jituwa.
Wannan dalili ne yasa hukumar ta HISBA ta ke kokarin sulhunta ma’aurata don su ci gaba da rayuwa cikin fahimtar juna tare da ‘ya’yansu.