Saturday, March 15
Shadow

Na rasa wace irin matace Sanata Natasha Akpoti, ta kawo mana korafi, ba’a gama bincike ba ta tsallaka ta kai kara kotu, ba’a gama shari’a ba ta sake tsallakewa ta kai korafi majalisar Dinkin Duniya>>Sanata Godswill Akpabio

Kakakin majalisar dattijai, Sanata Godswill Akpabio ya koka da irin halayyar Sanata Natasha Akpoti inda yace bai san wane irin tunani gareta ba.

Sanata Godswill Akpabio yace ta kawowa kwamitin da’a na majalisar dattijai korafi, ba’a gama bincike ba ta tafi ta kai kara kotu, can ma ba’a gama shari’a ba ta tafi ta kai korafi majalisar Dinkin Duniya.

Sanata Godswill Akpabio yace irin wannan abun ne zai iya sawa a daina baiwa mata mukaman siyasa.

Karanta Wannan  Karanta Abubuwa 10 da 'yan Najeriya suka fi kashe kudinsu akai yayin da ake cikin matsin rayuwa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *