Wednesday, May 21
Shadow

PDP ba ta shirya wa zaɓen 2027 ba – Wike

Ministan Abuja, Nyesom Wike ya ce babbar jam’iyyar hamayyar ƙasar, PDP ba ta da kyakkyawan shiri da tsarin kayar da APC a zaɓen 2027 ba.

Yayin da yake jawabi a wata ganawa da manema labarai a Abuja, ranar Juma’a, tsohon gwamnan na jihar Rivers ya ce a yanayin da jam’iyyar PDP ke ciki a halin yanzu ba za a ce ta shirya wa zaɓen 2027, saboda rikicin shugabanci da jam’iyyar ke ciki.

”PDP ba ta shirya wa zaɓen 2027 ba, wannan a bayyane yake. Ga yadda suke tafiya a yanzu rikicin jagoranci na ci gaba da yi wa jam’iyyar tarnaƙi”, in ji shi.

A baya-bayan nan dai wasu daga jam’iyyun hamayyar ƙasar ciki har da PDp na ƙoƙarin samar da wata haɗaka domin tunkarar APC a 2027.

Karanta Wannan  Ana ci gaba da kiraye-kirayen cewa Jihohin Arewa da suka bada hutun Ramadan a makarantu basu kyauta ba, inda Kungiyar Kiristocin CAN tace ko Saudi Arabia da UAE basu bayar da hutu a makarantu ba saboda Ramadan

To sai dai da alama tafiyar na ci gaba da fuskantar tasgaro, saboda muradun wasu ƴansiyasar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *