Saturday, December 13
Shadow

PDP ta bayyana yanda za’a yi a kayar da Tinubu karfe dayan rana a zaben 2027

Jam’iyyar PDP ta bayyana cewa hadakata tsakanin Atiku Abubakar da Peter Obi da Malam Nasiru Ahmad El-Rufai zai baiwa ‘yan adawa nasara akan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a zaben shekarar 2027.

Mataimakin shugaban matasa na jam’iyyar na kasa, Hon. Timothy Osadolor ne ya bayyanawa jaridar Vanguard hakan a wata ganawa da ta yi dashi.

Yace Musamman Atiku Abubakar da Peter Obi idan suka hade kaga ana da jimullar kuri’u Miliyan 13 kenan inda shi kuma shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ke da kuri’u Miliyan 8.

Yace a haka tun karfe dayan rana zasu kayar da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a ranar zabe.

Karanta Wannan  Kalli Hotuna: Mun cinye zaben shekarar 2027 mun gama>>Inji Ganduje Bayan da ya karbi 'yan NNPP da suka koma APC

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *