Friday, December 5
Shadow

Rundunar ƴansandan Abuja ta musanta garƙame hedikwatar PDP

Newly deployed Nigerian Formed Police Unit (FPU) personnel under the African Union Mission in Somalia (AMISOM) arrive at Aden Abdulleh International Airport, Mogadishu, Somalia on January 6, 2016. AMISOM Photo / Ilyas Ahmed

Rundunar ƴansandan Abuja ta musanta rahotannin da ke cewa jami’anta sun karɓe iko da hedikwatar jam’iyyar PDP ta Wadata Plaza a ranar Litinin.

Rundunar ta ce tana son “ta nuna cewa babu gaskiya a rahotonnin sannan ba haka al’amarin yake ba. An kai jami’an ƴansandan ne zuwa wurin taron domin wanzar da doka da oda kamar yadda tsarin mulki ya tanada.

A wata sanarwa, rundunar ta ce “babu wani lokaci da jami’an ƴansanda suka kulle sakateriyar jam’iyyar ta PDP.”

A sanarwar, kwamishinan ƴan sanda na Abujar ya buƙaci kafafen watsa labarai da su yi kaffa-kaffa wajen tantance labarai kafin su wallafa shi.

Karanta Wannan  Gwamna Abba Gida-gida ya raba fom din JAMB kyauta guda 10,000 ga ɗalibai

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *