Friday, December 26
Shadow

Rundunar ƴansandan Abuja ta musanta garƙame hedikwatar PDP

Newly deployed Nigerian Formed Police Unit (FPU) personnel under the African Union Mission in Somalia (AMISOM) arrive at Aden Abdulleh International Airport, Mogadishu, Somalia on January 6, 2016. AMISOM Photo / Ilyas Ahmed

Rundunar ƴansandan Abuja ta musanta rahotannin da ke cewa jami’anta sun karɓe iko da hedikwatar jam’iyyar PDP ta Wadata Plaza a ranar Litinin.

Rundunar ta ce tana son “ta nuna cewa babu gaskiya a rahotonnin sannan ba haka al’amarin yake ba. An kai jami’an ƴansandan ne zuwa wurin taron domin wanzar da doka da oda kamar yadda tsarin mulki ya tanada.

A wata sanarwa, rundunar ta ce “babu wani lokaci da jami’an ƴansanda suka kulle sakateriyar jam’iyyar ta PDP.”

A sanarwar, kwamishinan ƴan sanda na Abujar ya buƙaci kafafen watsa labarai da su yi kaffa-kaffa wajen tantance labarai kafin su wallafa shi.

Karanta Wannan  Ashe shima Godswill Akpabio ya taba sukar Bukola Saraki bayan da ya canja mai kujerar zama kamar yanda a yanzu fadanshi da Sanata Natasha Akpoti ya samo Asali ne daga canja mata kujera

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *