Thursday, May 29
Shadow

Saboda matsalar tsaro: Gwamnatin tarayya ta umarci ministan tsaro da shuwagabannin sojoji su koma Sokoto da zama

Gwamnatin tarayya ta umarci shuwagabannin sojoji da su koma jihar Sokoto da zama.

Hakan na zuwa ne yayin da matsalar tsaro musamman ta garkuwa da mutane ke kara kamari a yankin arewa maso yamma.

Sanarwar hakan na kunshene a cikin bayanan da sakataren yada labarai, Henshaw Ogubike ya fitar.

Yace wannan kokari ne na kawar da matsalar ta’addanci da garkuwa da mutane da sauran matsalolin tsaro da ake fama dasu a yankin.

Gwamnatin ta bayyana takaici da matsalar tsaron da ta ki ci ta ki cinyewa a yankin na Arewa maso yamma inda tace wannan mataki alamu ne na daukar matsalar da muhimmanci da gwamantin ta yi.

Karanta Wannan  A kokarin da masana kimiyya ke yi na Gano karshen Kasar da muke takawa, sun samu ci gaba inda suka yi nisa sosai a hakar da suke yi amma har yanzu basu kai karshen kasar ba

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *