Tuesday, February 24
Shadow

Saboda matsalar tsaro: Gwamnatin tarayya ta umarci ministan tsaro da shuwagabannin sojoji su koma Sokoto da zama

Gwamnatin tarayya ta umarci shuwagabannin sojoji da su koma jihar Sokoto da zama.

Hakan na zuwa ne yayin da matsalar tsaro musamman ta garkuwa da mutane ke kara kamari a yankin arewa maso yamma.

Sanarwar hakan na kunshene a cikin bayanan da sakataren yada labarai, Henshaw Ogubike ya fitar.

Yace wannan kokari ne na kawar da matsalar ta’addanci da garkuwa da mutane da sauran matsalolin tsaro da ake fama dasu a yankin.

Gwamnatin ta bayyana takaici da matsalar tsaron da ta ki ci ta ki cinyewa a yankin na Arewa maso yamma inda tace wannan mataki alamu ne na daukar matsalar da muhimmanci da gwamantin ta yi.

Karanta Wannan  Ban cewa Sheikh Dahiru Bauchi dan Whùtà ba sannan ban ce mai Kàfìrì ba>>Inji Baffa Hotoro, kwana daya bayan da aka makashi Kotu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *