Friday, December 5
Shadow

Satar Arziki ne zai kawo Trump Najeriya ba taimakon Kiristoci ba>>Inji Kungiyar Kare Muradun Yarbawa, Afenifere

Kungiyar Kare muradin yarbawa ta Afenifere ta bayyana cewa, shugaban kasar Amurka, Donald Trump zai shigo Najeriya ne da niyar satar arzikin kasa amma ba maganar tseratar da Kiristoci ba.

Kungiyar ta bakin sakataren yada labarinta, Mr. Jare Ajayi tace hujjar da Trump ya kawo ta banza ce kawai yana neman hanyar shigowa Najeriya ne.

Yace Trump na son amfani da wannan damar ne wajan tilasta Najeriya sayen abubuwa daga Amurka musamma makamai saboda baya jin dadin huldar da Najeriya ke yi da kasar China.

Yace sannan Amurkar ta ji haushin kalaman da mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima yayi a taron majalisar Dinkin Duniya inda ya goyi bayan kafa kasar Falasdiynawa.

Karanta Wannan  Ji labarin yanda wata mata ta danne yaro dan shekaru 5 ta yi lalata dashi, mahaifinsa yace ganin mazakutar dansa a mike yasa hankalinsa ya tashi

Kungiyar ta yi kira ga ‘yan Najeriya dama shuwagabannin da su kaucewa yin kalaman da zasu kara zhugha Amurka tace zata shigo Najeriya inda tace babu kasar da Amurka ta shiga da ta kare da samun zaman Lafiya.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *