
A jiyane Bidiyo ya bayyana inda aka ga Shugaban jam’iyyar APC, Dr. Abdullahi Umar Ganduje a tsaye, dansandansa ya duka yana daure masa takalmi.
Bidiyon ya watsu sosai a kafafen sada zumunta inda akaita bayyana mabanbanta ra’ayoyi akai.
Da yake mayar da martani kan lamarin ta bakin kakakinsa, Aminu Dahiru Ahmad, Ganduje yace wasu ne dake son jawo cece-kuce da kawo rudani a tsakanin al’umma suka fitar da Bidiyon.
Yace Ganduje an sanshi mutum ne me haba-haba da mutane sannan kuma yana da kyakkyawar alaka tsakaninsa da masu masa aiki shiyasa aka ga abinda dansandan yayi.